Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw
Published: January 19, 2026 at 7:23 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 19, 2026

Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta dakatar da kocin Senegal Pape Thiaw bayan ya yi abin da bai dace ba a wasan karshe na AFCON 2025 tsakanin Senegal da Morocco masu masaukin baki.

Kwamitin ladabtarwa na CAF ya sami Thiaw da laifin karya dokokin gasar bayan ya umarci ‘yan wasansa da su fice daga filin wasa don nuna rashin amincewa kan hukuncin da alkali yaye mai cike da ce-ce-ku-ce a karshen wasan.

Kodayake Senegal ta dawo fili don kammala wasan kuma ta samu nasara 1-0 bayan karin lokaci, CAF ta bayyana matakin da mai horaswar ya dauka a matsayin abin da ba za a amince da shi ba don yana lalata martaban kwallon kafa ta Afirka.

Hukuncin ya zo ne bayan bincike mai zurfi da ya mamaye wasan, duk da cewa Senegal ta dauki kofin.

CAF ta tabbatar a cikin wata sanarwa cewa Thiaw zai fuskanci dakatarwa daga dukkan gasannin CAF, tare da karin takunkumi ciki har da tara.

Tsawon lokacin haramcin yana nufin Senegal za ta kasance ba tare da kocinta ba a wasannin gasa masu zuwa, wanda hakan ya tilasta wa FA ta Senegal yin la’akari da shirye-shiryen neman kocin wucin gadi.

CAF ta jaddada kudurinta na yin da’a da kuma girmama jami’an wasa a duk gasannin da take yi, tana mai lura da cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ya fi ƙarfin dokoki.

Hukumar gudanarwa ta ƙara da cewa an sanya takunkumin da ya dace bisa ga dokokin ladabtarwa kuma ta yi gargaɗin cewa sake maimaita irin wannan hali a nan gaba zai jawo ƙarin hukunci mai tsanani.

Wannan lamari ya haifar da muhawara mai zafi a faɗin Nahiyar Afirka da haifar da damuwa game da alkalanci, ƙa’idoji, da’a, da kuma ɗabi’u a manyan gasannin Afirka.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland
Next Post: Barcelona na hangen Enrique Ko Arteta

Karin Labarai Masu Alaka

Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
  • Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Ukraine Takai Hari Wajen Kera Makami Mai Linzami A Rasha Labarai
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.