Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta dakatar da kocin Senegal Pape Thiaw bayan ya yi abin da bai dace ba a wasan karshe na AFCON 2025 tsakanin Senegal da Morocco masu masaukin baki.

Kwamitin ladabtarwa na CAF ya sami Thiaw da laifin karya dokokin gasar bayan ya umarci ‘yan wasansa da su fice daga filin wasa don nuna rashin amincewa kan hukuncin da alkali yaye mai cike da ce-ce-ku-ce a karshen wasan.
Kodayake Senegal ta dawo fili don kammala wasan kuma ta samu nasara 1-0 bayan karin lokaci, CAF ta bayyana matakin da mai horaswar ya dauka a matsayin abin da ba za a amince da shi ba don yana lalata martaban kwallon kafa ta Afirka.
Hukuncin ya zo ne bayan bincike mai zurfi da ya mamaye wasan, duk da cewa Senegal ta dauki kofin.
CAF ta tabbatar a cikin wata sanarwa cewa Thiaw zai fuskanci dakatarwa daga dukkan gasannin CAF, tare da karin takunkumi ciki har da tara.
Tsawon lokacin haramcin yana nufin Senegal za ta kasance ba tare da kocinta ba a wasannin gasa masu zuwa, wanda hakan ya tilasta wa FA ta Senegal yin la’akari da shirye-shiryen neman kocin wucin gadi.
CAF ta jaddada kudurinta na yin da’a da kuma girmama jami’an wasa a duk gasannin da take yi, tana mai lura da cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ya fi ƙarfin dokoki.
Hukumar gudanarwa ta ƙara da cewa an sanya takunkumin da ya dace bisa ga dokokin ladabtarwa kuma ta yi gargaɗin cewa sake maimaita irin wannan hali a nan gaba zai jawo ƙarin hukunci mai tsanani.
Wannan lamari ya haifar da muhawara mai zafi a faɗin Nahiyar Afirka da haifar da damuwa game da alkalanci, ƙa’idoji, da’a, da kuma ɗabi’u a manyan gasannin Afirka.


