Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa
Published: January 21, 2026 at 5:38 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomi a kasar Togo sun kame tare da korar tsohon shugaban kasar Burkina Faso, Paul Henri Damiba, zuwa kasar sa ta haihuwa, bayan da gwamnati ta zarge shi da laifin yunkurin juyin mulki, kamar yadda wasu majiyoyi 2 suka shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar Talata.

Paul Henri Damiba, ya karbi ragamar mulki ne a shekarar 2022, bayan da aka yiwa gwamnatin farar hula ta Burkina faso juyin mulki, wadda farin jinin ta ya dusashe saboda yawan tashin hankali da ake samu daga ‘yan ta’adda.

Rashin nasarar Damiba wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda, ya haifar da fushin sojin kasar, abinda ya jawo shima aka tsige shi a wannan shekarar, a wani juyin mulki karkashin Ibrahim Traore, wanda a yanzu shi ne shugaban kasar karkashin mulkin soja.

A farkon Wannan watan ne Burkina Faso ta sanar cewa ta dakile wani yunkuri na kashe shugaba Traore, da ake zargin Damiba ne ya shirya, wanda ya nemi mafaka a Lome, babban birnin kasar Togo.

Wani jami’in tsaro da wani dake da kusanci da shugaban kasar Togo sun shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters ranar Talata cewa An kama Damiba ranar Asabar, kuma An dauke shi a jirgi zuwa Ouagadougou, babban birnin Burkina Faso.

Togo ta tabbatar da fitar da Damiba daga kasar, inda ta ce ta yi haka ne, bisa bukata daga Burkina Faso.

Laifukan da ake tuhumar Damiba a Burkina Faso da su sun hada da almubazzaranci da wadaka da kudaden al’umma da halarta kudin haram, a cewar gwamnatin Togo

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama
Next Post: Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.