Jami’an tsaro a Nigeria sun yi nasarar kubutar da mutane 62 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su, a wasu hare-hare da suka kai jihohin Kebbi da Zamfara, a yunkurin su na dakile barazanar ‘yan ta’addan a arewa maso gabashin kasar, a cewar sojojin a ranar laraba
Mai magana da yawun sojojin laftanal kanal Olaniya Osoba, ya ce dakarun su sun kai farmaki wata sananniyar maboya ta ‘yan ta’adda a jihar Zamfara, bayan da suka samu rahoton cewa akwai mutanen da ake tsare da su a can.
Sojojin sun ce an kubutar da dukkanin mutanen da aka yi garkuwa da su, su 62, kuma suna nan cikin kulawa da tsaro, kafin daga bisani a hada su da ‘yan uwan su.
A wani samamen kuma da Sojoji suka kai, sun yi nasarar wargaza wasu ‘yan kungiyar ‘yan ta’adda na Lakurawa a garin Augie, wanda ya ke kusa da iyakar Kebbi da Sokoto.


