Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano
Published: January 22, 2026 at 5:51 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata gobara da ta tashi a ranar Litinin ta ƙone ajujuwan karatu 34 a wata makarantar kiwon lafiyar dabbobi da ke karamar hukumar Kabo a jihar Kano.

A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kashe gobara ta ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2:53 na rana.

Sanarwar ta ce dakin kula da gobara na hukumar ya karɓi kiran taimako daga wani Jamilu Abubakar, wanda ya ba da rahoton tashin gobara a cikin makarantar. Nan da nan aka tura ma’aikatan kashe gobara daga tashar Rijiyar Zaki zuwa wurin da lamarin ya faru.

“Da suka iso wurin, ma’aikatanmu sun gano wani ginin bene na ƙasa mai fadin ƙafa 500 da tsayin ƙafa 500, da ake amfani da shi a matsayin wajen kiwon lafiyar dabbobi, yana ƙonewa cikin wuta,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa dakuna 16 sun lalace sosai, yayin da wasu 18 suka samu lalacewar ɓangare-ɓangare saboda gobarar.

Sai dai an samu nasarar dakile wutar, inda aka hana ta yaɗuwa zuwa sauran dakuna da ofisoshi a cikin cibiyar.

“An tura motar kashe gobara guda ɗaya daga tashar Rijiyar Zaki don dakile lamarin, in ji sanarwar, wadda ta danganta nasarar aikin da saurin martanin ma’aikatan kashe gobara.

Ba a samu rahoton mutuwar kowa ba a lokacin da ake rubuta wannan rahoto, yayin da ba a bayyana musabbabin gobarar ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai
Next Post: Bassirou: Tawagar Senegal Zasu Samu Kyautar Kudi Da Filaye Sakamakon Nasarar Da sukayi AFCON 2025

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
  • Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
  • Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC Shirye-Shirye
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
  • Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.