Gwamnatin jihar Gombe ta bai wa Ƙungiyar Maharba da Ƙungiyar Yan Sintiri ta Najeriya (VGN) motoci na aiki, a wani mataki na ƙarfafa ayyukan tsaro da kuma inganta tsaron al’umma a faɗin jihar.
Tallafin ya haɗa da bai wa Ƙungiyar Maharban jihar Gombe motoci biyu kirar Toyota Hilux, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Rabiu Baushe (Baushen Gombe), da kuma bai wa Ƙungiyar Yan Sintiri ta Najeriya (VGN), ta jihar Gombe, mota ɗaya kirar Toyota Hilux, ƙarƙashin jagorancin Abubakar Yaro.
Da yake miƙa motocin a madadin Gwamnatin jihar, Darakta-Janar kuma Kwamandan Hukumar Tsaro, Zirga-zirga da Kare Muhalli ta jihar Gombe (GOSTEC)/Operation Hattara, ACP Ibrahim Bappah (Rtd), ya bayyana cewa an bayar da tallafin ne domin ƙarfafa tsaron cikin gida ta hanyar Operation Hattara, tare da zurfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da ƙungiyoyin tsaron al’umma wajen tinkarar ƙalubalen tsaro.

A cewarsa, bayar da motocin na daga cikin tsare-tsaren Gwamnatin jihar Gombe na ƙara wa waɗannan ƙungiyoyi ƙarfi da karsashi wajen gudanar da ayyukansu, da kuma bunƙasa haɗin gwiwar hukumomi domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar.

“An bai wa shugabannin waɗannan ƙungiyoyi motocin ne domin ƙara musu ƙarfin aiki da kuma tallafa wa ƙoƙarin bai ɗaya na kare rayuka da dukiyoyi a faɗin Jihar Gombe,” in ji ACP Bappah.
Ya kuma yaba wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, bisa jajircewarsa wajen inganta tsarin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.
ACP Bappah ya bayyana tallafin a matsayin wanda ya zo a kan lokaci kuma mai muhimmanci, inda ya ce motocin za su taimaka wajen ƙara saurin kai ɗauki, inganta zirga-zirga, da kuma ƙara ingancin ayyukan tsaro, musamman a matakin ƙananan hukumomi.
A nasa ɓangaren, shugabannin ƙungiyoyin da suka amfana da tallafin sun gode wa Gwamnatin jihar Gombe bisa wannan tallafi, tare da yin alƙawarin amfani da motocin yadda ya dace, bisa ƙa’idoji da dokoki, domin ayyukan tsaro kaɗai.
Sun kuma tabbatar da cewa tallafin zai ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakaninsu da sauran hukumomin tsaro, domin tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da tsaron lafiyar al’ummar jihar Gombe.


