Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana Bikin Kamun Kifi da Bajekolin Al’adun Duniya na Argungu a matsayin wata babbar alama ta haɗin kan Najeriya, gadon al’adu, da kuma karɓuwar al’adun ƙasar nan a idon duniya, yayin da ta jaddada muhimmancin sa wajen bunƙasa tattalin arziki ta hanyar yawon buɗe ido.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar buɗe taron bikin Argungu karo na 61, wanda aka gudanar a ranar Laraba, 21 ga Janairu, 2026, a dandalin hedikwatar Hukumar Talbijin na Ƙasa (NTA) da ke Abuja.
Daraktan Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar, Dakta Suleiman Haruna, shi ne ya wakilci Ministan a wurin taron.
A cewar Ministan, bikin Argungu na ɗaya daga cikin tsofaffin bukukuwan al’adun gargajiya mafi daɗewa a Najeriya, wanda tun farkon kafuwar sa a shekarar 1934 yake haɗa kan al’umma cikin zaman lafiya da manufa ɗaya.


