Chief Muhoozi Kainerugaba, shugaban dakarun sojojin Uganda, kuma da ga shugaba Yoweri Museveni, ya ce hukumomin kasar suna tsare da magoya bayan jam’iyyun adawa 2000, tare da hallaka 30, kuma suna farautar wasu, biyo bayan zaben shugaban kasa da ake kalubalantar nasarar Yoweri Musaveni.
Yoweri Museveni, ya rike ragamar mulkin kasar har kusan tsawon shekaru 40. A zaben da aka gudanar ranar 15 ga Watan Janairun nan ma, hukumar zabe ta ce shi yaci zaben, inda ya bawa babban dan adawa Bobi Wine na jam’iyyar National Unity Platform, wato NUP tazara sosai wajen yawan kuri’u.
Bobi Wine, wanda da mawaki ne, ya zamo dan siyasa, kuma sunan sa na asali Robert Kyagulanyi, ya ki amincewa da sakamakon zaben, inda yayi zargin an tafka magudi, kuma daga nan ya shiga buya.
A wasu sakonni da ya wallafa a shafin sada zumunta cikin dare shugaban dakarun sojojin na Uganda, kuma da ga Museveni, ya bayyana yadda aka gudanar da kame tare da kashe wasu magoya bayan jam’iyyar NUP, inda ya alakanta su da bata gari, kuma ‘yan ta’adda.
Gwamnati ta zargi Magoya bayan Wine da tada hargitsin zabe, shi kuma a nasa bangaren ya ce jami’an tsaro ne suka far ma magoya bayan nasu. Kamfanin dillacin labarai na Reuters bai samu damar samun sahihancin wadannan zarge-zarge ba.


