Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin gyara hanyar Akwanga a jihar Nasarawa zuwa Jos a jihar Filato.

Shugaban kasar yayi wannan alkawari ne yayin karbar gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang wanda ya chanza sheka daga jami’iyyar PDP zuwa jami’iyyar APC mai mulki a Najeriya.
Dubban jama’a ne, musamman ‘ya’yan jami’iyyar APC da suka hada da shugaban majalisar dattawan Najeriya, sanatoci, shugaban majalisar wakilai da ‘yan majalisar, gwamnoni da shugabannan APC daga matakin kasa zuwa jaha da kananan hukumomi ne suka yi cincirindo a Jos, don nuna goyon baya wa gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang daya shiga jami’iyyar APC.
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu wanda mataimakinsa sanata Kashim Shettima ya wakilta a wurin taron, ya fara ne da yabawa Gudunmawar da wassu ‘ya’yan jahar Filato da suka hada da Janar Yakubu Gowon, Marigayi Solomon Lar, Marigayi Jeremiah Useni da sauransu, suka bayar wajen gina Najeriya da hada kan kasar da ma sadaukar da kai da suka yi a bangaren siyasa.
Mataimakin shugaban kasar yace nan da makonni uku, dan kwangila zai fara gudanar da aikin hanyar Akwanga zuwa Jos.

A nasa jawabin, gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang yace shugaban kasa Bola Tinubu ne ya gayyato shi shiga jami’iyyar APC, kuma ya amince ne saboda ya lura da aniyarsa ta sanya fasalin Najeriya don maida ita kan turbar hadin kai da ci gaba.
Gwamnan na jahar Filato, Caleb Mutfwang yace wadansu na cewa mun sauya sheka, sam ba haka bane, muna sake daidaitawa da samadda dabarun samun romon damokradiyya ne wa jahar Filato.
Da yake mika wa gwamnan tutar APC da tsintsiya, shugaban jami’iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda yace tsintsiyar zata share rarrabuwar kawuna, ta kuma share rashawa ta kuma samadda hadin kai.
Shugaban jami’iyyar ta APC yace ‘’ina tabbatar maka, Caleb Mutfwang, zaka dawo gidan gwamnati a matsayin gwamna a shekara ta dubu biyu da ishirin da bakwai, don zamu baka goyon baya.’’
Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya yi addu’a ne da daukan matakan mai da ‘yan gudun hijira a jahar Filato zuwa gidajensu.
Shugaban majalisar dattawan yace, ina so in shaida maka cewa majalisar tarayya zata tattauna kan matakan samadda kudade da zai baka damar mai da jama’ar ka dake sansanonin gudun hijira zuwa kauyukan su.
Gwamnan jahar Nasarawa, Abdullahi Sule, wanda shine shugaban majalisar gwamnonin Arewa tatsakiya yace a yanzu dukkan gwamnonin shiyyar suna jami’iyya daya.
Abdullahi Sule yace ‘’saboda mun yi imanin APC itace amintacciyar jami’iyya dake da kyakkyawar tawaga ta Bola Tinubu da Kashim Shettima kuma suna da goyon baya mai karfi daga Arewa ta tsakiya.
Gwamnonin jahohin Lagos, Katsina, Borno, Edo, Ebonyi Sokoto da Taraba ne suka halarci taron, yayinda mataimakin gwamnan jahar Gombe da wassu jahohin suka wakilci gwamnoninsu.
A yanzu dai gwamnoni ishirin da tara ne daga cikin talatin da shida a fadin Najeriya ke jami’iyyar APC, a daidai lokacin da jami’iyyar ta sha alwashin mai da Najeriya kasa mai jami’iyya daya.
Daga Jos Ga Rahoton Zainab Babaji


