Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos
Published: January 27, 2026 at 10:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 27, 2026

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin gyara hanyar Akwanga a jihar Nasarawa zuwa Jos a jihar Filato.

Shugaban kasar yayi wannan alkawari ne yayin karbar gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang wanda ya chanza sheka daga jami’iyyar PDP zuwa jami’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Dubban jama’a ne, musamman ‘ya’yan jami’iyyar APC da suka hada da shugaban majalisar dattawan Najeriya, sanatoci, shugaban majalisar wakilai da ‘yan majalisar, gwamnoni da shugabannan APC daga matakin kasa zuwa jaha da kananan hukumomi ne suka yi cincirindo a Jos, don nuna goyon baya wa gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang daya shiga jami’iyyar APC.

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu wanda mataimakinsa sanata Kashim Shettima ya wakilta a wurin taron, ya fara ne da yabawa Gudunmawar da wassu ‘ya’yan jahar Filato da suka hada da Janar Yakubu Gowon, Marigayi Solomon Lar, Marigayi Jeremiah Useni da sauransu, suka bayar wajen gina Najeriya da hada kan kasar da ma sadaukar da kai da suka yi a bangaren siyasa.

Mataimakin shugaban kasar yace nan da makonni uku, dan kwangila zai fara gudanar da aikin hanyar Akwanga zuwa Jos.

A nasa jawabin, gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang yace shugaban kasa Bola Tinubu ne ya gayyato shi shiga jami’iyyar APC, kuma ya amince ne saboda ya lura da aniyarsa ta sanya fasalin Najeriya don maida ita kan turbar hadin kai da ci gaba.

Gwamnan na jahar Filato, Caleb Mutfwang yace wadansu na cewa mun sauya sheka, sam ba haka bane, muna sake daidaitawa da samadda dabarun samun romon damokradiyya ne wa jahar Filato.

Da yake mika wa gwamnan tutar APC da tsintsiya, shugaban jami’iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda yace tsintsiyar zata share rarrabuwar kawuna, ta kuma share rashawa ta kuma samadda hadin kai.

Shugaban jami’iyyar ta APC yace ‘’ina tabbatar maka, Caleb Mutfwang, zaka dawo gidan gwamnati a matsayin gwamna a shekara ta dubu biyu da ishirin da bakwai, don zamu baka goyon baya.’’

Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya yi addu’a ne da daukan matakan mai da ‘yan gudun hijira a jahar Filato zuwa gidajensu.

Shugaban majalisar dattawan yace, ina so in shaida maka cewa majalisar tarayya zata tattauna kan matakan samadda kudade da zai baka damar mai da jama’ar ka dake sansanonin gudun hijira zuwa kauyukan su.

Gwamnan jahar Nasarawa, Abdullahi Sule, wanda shine shugaban majalisar gwamnonin Arewa tatsakiya yace a yanzu dukkan gwamnonin shiyyar suna jami’iyya daya.

Abdullahi Sule yace ‘’saboda mun yi imanin APC itace amintacciyar jami’iyya dake da kyakkyawar tawaga ta Bola Tinubu da Kashim Shettima kuma suna da goyon baya mai karfi daga Arewa ta tsakiya.

Gwamnonin jahohin Lagos, Katsina, Borno, Edo, Ebonyi Sokoto da Taraba ne suka halarci taron, yayinda mataimakin gwamnan jahar Gombe da wassu jahohin suka wakilci gwamnoninsu.

A yanzu dai gwamnoni ishirin da tara ne daga cikin talatin da shida a fadin Najeriya ke jami’iyyar APC, a daidai lokacin da jami’iyyar ta sha alwashin mai da Najeriya kasa mai jami’iyya daya.

Daga Jos Ga Rahoton Zainab Babaji

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260127-WA0041.mp3

 

Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar
Next Post: An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau Afrika
Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
Isra’ila Ta Kai Hari Cibiyar Makamashin Nukiliyar Iran Afrika
Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
  • Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
  • An Kaddamar Da Rigakafin Cutar HIV AIDS A Kasar Zimbabwe Kimiya
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.