Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu
Published: January 28, 2026 at 11:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan uwan wasu mutane 2 da aka kashe sakamakon harin da sojin Amurka suka kai wani jirgin ruwa da ake zaton na dauke da muggan kwayoyi, da ya taso daga Venezuela sun kai kara gaban kotu kan yiwa ‘yan uwan nasu kisan sakaci ranar Talata. Sun yi ikirarin cewa an kashe ‘yan uwan nasu ne ta hanyar da ta sabawa doka, ta yadda sojoji ke harin jiragen ruwan farar hula.

Lawyoyin masu rajin kare hakki, sun gabatar da karar ne a wata babban kotun kasa ta Amurka da ke birnin Boston. Karar da ta kasance ta farko da aka gabatar tun tun da Amurka ta kai hari har sau 36 kan jiragen ruwa a tekun Carribean da na Pacific, bisa umarnin gwamnatin Donald Trump, abinda yayi sanadiyyar rayuka 126 tun watan Satumbar bara.

‘Yan uwan Chad Joseph da Rishi Samaroo, mutane biyu ‘yan kasar Trinidad, na daga cikin mutane 6 da aka kashe a wani hari da aka kai ranar 14 ga Watan Oktoba. karar da aka gabatar ta ce mutanen biyu suna noma ne da kamun kifi a Venezuela, kuma suna hanyar su ta komawa gida ne a Las Cuevas da ke Trinidad yayin da aka kai musu harin.

Lauyan masu gabatar da kara Brett Max na ofishin masu rajin kare hakki na American Civil Liberties Union, ya ce wannan kisa ne da bashi da hujja daga gwamnatin dake cin zarafin ikon mulki ba tare da fuskantar hukunci ba, kuma wannan kara da aka gabatar na bukatar bin hakki da kuma kare dokokin shari’a.

Kungiyar lauyoyin rajin kare hakki sun gabatar da karar ne karkashin dokar Mutuwa a Teku mai Zurfi (wato Death on High Seas Act) a turance, dokar da ta bawa ‘yan uwan mamata damar kai kara don kisan sakaci ga ‘yan uwan su da ya auku a babban teku ko teku me zurfi, da kuma dokar kisa ga baki (Alien Tort Statute), ta shekarar 1789, wadda ta bawa bakin haure damar kai kara gaban kotunan Amurka, idan Amurkan ta saba dokar kasa da kasa.

Mahaifiyar Chad Joseph, Lenore Burnley, da kuma ‘yar uwar Rishi Samaroo, Sallycar Korasingh ne suka kai karar, kuma suna neman diyya ne kawai daga gwamnatin Amurka kan kisan ‘yan uwan nasu, ba wai kotu ta bada umurnin hana kara kai hare-haren nan gaba ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka
Next Post: Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki Kiwon Lafiya
  • Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
  • An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi Labarai
  • Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.