Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu
Published: January 28, 2026 at 11:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan uwan wasu mutane 2 da aka kashe sakamakon harin da sojin Amurka suka kai wani jirgin ruwa da ake zaton na dauke da muggan kwayoyi, da ya taso daga Venezuela sun kai kara gaban kotu kan yiwa ‘yan uwan nasu kisan sakaci ranar Talata. Sun yi ikirarin cewa an kashe ‘yan uwan nasu ne ta hanyar da ta sabawa doka, ta yadda sojoji ke harin jiragen ruwan farar hula.

Lawyoyin masu rajin kare hakki, sun gabatar da karar ne a wata babban kotun kasa ta Amurka da ke birnin Boston. Karar da ta kasance ta farko da aka gabatar tun tun da Amurka ta kai hari har sau 36 kan jiragen ruwa a tekun Carribean da na Pacific, bisa umarnin gwamnatin Donald Trump, abinda yayi sanadiyyar rayuka 126 tun watan Satumbar bara.

‘Yan uwan Chad Joseph da Rishi Samaroo, mutane biyu ‘yan kasar Trinidad, na daga cikin mutane 6 da aka kashe a wani hari da aka kai ranar 14 ga Watan Oktoba. karar da aka gabatar ta ce mutanen biyu suna noma ne da kamun kifi a Venezuela, kuma suna hanyar su ta komawa gida ne a Las Cuevas da ke Trinidad yayin da aka kai musu harin.

Lauyan masu gabatar da kara Brett Max na ofishin masu rajin kare hakki na American Civil Liberties Union, ya ce wannan kisa ne da bashi da hujja daga gwamnatin dake cin zarafin ikon mulki ba tare da fuskantar hukunci ba, kuma wannan kara da aka gabatar na bukatar bin hakki da kuma kare dokokin shari’a.

Kungiyar lauyoyin rajin kare hakki sun gabatar da karar ne karkashin dokar Mutuwa a Teku mai Zurfi (wato Death on High Seas Act) a turance, dokar da ta bawa ‘yan uwan mamata damar kai kara don kisan sakaci ga ‘yan uwan su da ya auku a babban teku ko teku me zurfi, da kuma dokar kisa ga baki (Alien Tort Statute), ta shekarar 1789, wadda ta bawa bakin haure damar kai kara gaban kotunan Amurka, idan Amurkan ta saba dokar kasa da kasa.

Mahaifiyar Chad Joseph, Lenore Burnley, da kuma ‘yar uwar Rishi Samaroo, Sallycar Korasingh ne suka kai karar, kuma suna neman diyya ne kawai daga gwamnatin Amurka kan kisan ‘yan uwan nasu, ba wai kotu ta bada umurnin hana kara kai hare-haren nan gaba ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka
Next Post: Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Nanata Aniyar Mallakar Greeland Daga Kasar Denmark Amurka
  • Pads To Prosperity: NEDC Ta Horar Da Mata 280 Kan Kera Pads A Gombe Afrika
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • Afirka Ta Kudu Zata Fuskanci Koma Baya A Bangaren Samar Da Ayyukanyi Afrika
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.