A gabas ta tsakiya kuma, Shugaban Amurka Donald Trump, ya fadawa manema labarai a fadar White House ranar Litinin cewa, Washington da Iran suna ci gaba da gudanar da shawarwari, yayinda manyan jiragen yaki na ruwan Amurka suke kara zuwa yankin inji Mr. Trump.
A halinda ake ciki kuma, rahotanni suna nuni da cewa mahukunta a Tehran suna kara nuna damuwa sosai cewa duk wani hari daga Amurka zai sake tunzura masu zanga zanga a kasar da suka hau kan tituna, kuma wannan karon saboda mummunar matakin murkushe masu zanga zangar da hukumomin kasar suka yi a baya bayan nan, mutane sun fusata wadda ya kawar da duk wani tsoro. Akwai alamun jama’ar kasar yanzu a shirye suke su tunkari jami’an tsaro.
Rahoton yace wannan mataki zai kai ga rushewar gwamnati, kamar yadda wasu majiyoyi suka ce an gayawa shugaban addinin kasar Ayatollahi Ali Khamei a zaman shawarwari da suka yi.
Daya daga cikin jami’an kasar ya gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, makiyan Iran suna son ganin karin zanga zanga domin kawo karshen gwamnatin kasar mai bin tafarkin Islama, yace idan haka ta faru abun takaici ne domin hakan zai haifar da tarzoma idan zanga zanga ta sake barkewa.


