Kimanin mutane 30 ne ake fargabar sun mutu tare kona gidan wani basarake asakamakon wani mummunan harin da wasu yanbindiga suka kai a Jihar Kwara dake tarayyar Najeriya,
Rahotanni daga yankin woro na karamar Hukumar kayama ta jihar Kwaran wanda yake kan iyakar jihohin kwara da Neja na nuna cewa maharan sun bankawa garin wuta tare da harbe harben bindiga irin na mai kan uwa da wabi,
Wani mazaunin karin kayama da ya bukaci a sakaya sunanshi yace ya zuwa lokacin da muke magana dashi mutanen garin na wuro sun tarwatse sun shiga daji yayinda wasu Kuma ke boye a wasu wuraren kamar yadda yayi Karin bayani…
Kawowa lokacin hada wannan rahoto dai kokarin samun rundunar yansanda na Jihar kwaran yaci tura,
To dan majalisar dokoki ta jihar Kwaran Mai wakiltar karamar hukumar kayama a Majalisar Jihar Kwaran Hon.Baba Ahmed kayama ya tabbatar da Aukuwar Lamarin Amma yace ya zuwa lokacin da muke magana dashi basu tan tance yawan wadanda suka rasa rayukkansu ba..
Ayanzu Jihar kwaran na ci gaba da fuskantar wannan matsala ta yanbindiga Lamarin dake kara jefa mazauna Jihar cikin Yanayi na zullumi tare da nuna bukatar ganin hukumomi sun Dauki Matakin dakeleshi.

