Shugaban kungiyar ‘yan tawayen AFC da M23 Jamhuriyar Demokradiyar Congo, ya wallafa a shafin sa na sada zumunta cewa sune suka kai harin jirgi mara matuki na drone a filin jirgin saman Kisangani dake arewa maso gabashin kasar.
Gwamnatin Lardin Tshopo, inda garin na Kisangani yake, ta ce jiragen drone shake da bama bamai sun hankoro filin jirgin saman na Kisangani ne.
A wani sako da ya wallafa a shafin sa na X, shugaban ‘yan tawayen, Corneilli Nangaa ya ce, wannan harin ya nuna rundunar sojan Congo, yanzu basu da wani fifiko a yakin sama.


