Farfesa Muhammad Inuwa Ja’afaru ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Tarayya dake Kashere a jihar Gombe dake arewa maso gabashin Najeriya
A wani muhimmin sauyi na jagoranci da ke nuna sabon babi a tafiyar Sashin ilimin, cikin saƙon taya murna da fatan alheri, an bayyana cewa ana sa ran sabon Shugaban Jami’ar zai kawo ƙwarewa, hangen nesa da ƙuduri wajen inganta harkokin koyarwa, bincike da hidimtawa al’umma, tare da ƙarfafa tsarin gudanarwa mai gaskiya da rikon amana.

Sanarwar Mataimakin Jami’an yada labaran Jami’ar Hassan Abubakar Kwami ta nuna Cewa, Masu ruwa da tsaki sun bayyana fatan cewa jagorancinsa zai ƙara ɗaga darajar jami’ar a matakin ƙasa da ƙasa, tare da bunƙasa haɗin gwiwa da sauran cibiyoyin ilimi da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Haka kuma, an miƙa saƙon godiya ga tsohon Shugaban Jami’ar Ferfsa Umaru Pate bisa rawar da ya taka wajen tafiyar da al’amuran jami’ar, tare da addu’ar Allah Ya ba shi nasara da dacewa a matakan rayuwarsa na gaba.


