Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi
Published: February 14, 2026 at 4:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta ce tana ci gaba da tuntuba kan jadawalin babban zaɓen 2027, bayan da aka nuna damuwa cewa ranar zaɓen ta yi daidai da watan Ramadan.

A wata sanarwa da Kwamishinan Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Zaɓe, Mohammed Haruna, ya fitar, hukumar ta ce an tsara ranakun ne bisa tanadin Kundin Tsarin Mulki na 1999 da dokar zaɓe ta 2022 da kuma ƙa’idojin INEC.

INEC ta sanya 20 ga Fabrairu, 2027 domin zaɓen Shugaban Ƙasa da na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, yayin da zaɓen gwamnoni da na majalisun dokokin jihohi zai gudana a 6 ga Maris, 2027.

Sai dai wasu ‘yan Najeriya, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, sun buƙaci a sake duba ranakun, suna mai cewa sun faɗa cikin watan azumi, wanda ka iya shafar yawan fitowar masu zaɓe.

Haruna ya ce hukumar na duba lamarin, kuma idan buƙatar hakan ta taso, za ta nemi matakin Majalisa domin tabbatar da gudanar da zaɓe mai haɗa kowa da kowa.

Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata
Next Post: Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2 Sauran Duniya
  • Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.