Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi
Published: February 14, 2026 at 4:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta ce tana ci gaba da tuntuba kan jadawalin babban zaɓen 2027, bayan da aka nuna damuwa cewa ranar zaɓen ta yi daidai da watan Ramadan.

A wata sanarwa da Kwamishinan Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Zaɓe, Mohammed Haruna, ya fitar, hukumar ta ce an tsara ranakun ne bisa tanadin Kundin Tsarin Mulki na 1999 da dokar zaɓe ta 2022 da kuma ƙa’idojin INEC.

INEC ta sanya 20 ga Fabrairu, 2027 domin zaɓen Shugaban Ƙasa da na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, yayin da zaɓen gwamnoni da na majalisun dokokin jihohi zai gudana a 6 ga Maris, 2027.

Sai dai wasu ‘yan Najeriya, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, sun buƙaci a sake duba ranakun, suna mai cewa sun faɗa cikin watan azumi, wanda ka iya shafar yawan fitowar masu zaɓe.

Haruna ya ce hukumar na duba lamarin, kuma idan buƙatar hakan ta taso, za ta nemi matakin Majalisa domin tabbatar da gudanar da zaɓe mai haɗa kowa da kowa.

Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata
Next Post: Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana
  • INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi
  • Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa
  • Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
  • An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
  • Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.