Rundunar sojin Nigeria ta yi nasarar dakile wasu hare-haren ‘yan ta’adda kan sansanin sojoji biyu a jihar Borno, da yayi sanadiyyar hallaka sojoji a wurin, a cewar rundunar sojin a yau Litinin.
Harin da aka kai a karshen mako, ya je kan sansanin soji na Pulka da ke da iyaka da kasar Cameroon da kuma Mandaragirau a kudancin Borno.
Mai magana da yawun sojojin Sani Uba, ya ce kungiyar ‘yan ta’adda na ISWAP sun kai harin ne kan babura da bindigogi, amma sojojin su da suka kwan da zaton akwai yiwuwar kai harin sun mai da musu da wuta mai tsanani.


