Mutumin da shugaban Amurka Donald Trump ya nada jakadan kasar a Afirka ta kudu, dan gwagwarmaya mai ra’ayin mazan jiya Leo Brent Bozell na uku, wanda kuma marubuci ne ya sauka kasar, inda zaiyi aiki domin gyara dangantaka tsakanin kasashen biyu wanda yayi tsami.
Wani jami’i a ofishin jakadancin Amurka ya fadawa kamfanin dilancin labarai na Reuters cewa, Ambasda Bozell ya iso. Kuma ana sa ran zai gabatarwa shugaba Cyril Ramaphosa takardunsa gabannin ya fara aiki.
Dangantaka tsakanin hukumomi a Washington da Pretoria sunyi baya ainun bara, yayinda Trump yake sukar kasar cewa tana muzgunawa tsiraru farar fata, ya soki mu’amalar kasar da Rasha da kuma China, sannan ya aza mata haraji mai yawa kan kayayyaki daga kasar.
Afirka ta kudu bada ta da jakada a Washington tun cikin watan Yunin bara, bayanda shugaba Trump ya kori jakadan Afirka ta kudu Ibrahim Rasool, daga kasar.
A lokacin da ake tantance shi cikin watan Oktoban bara, Ambasada Bozell yace zai tunkari aikinsa tare da girmamawa ga al’umar Afirka ta kudu, kuma yana ganin akwai damar kulla dangantaka mai dorewa duk da cewa akwai sassan da suke da sabanin ra’ayi.


