Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta bada da umarnin rufe dukkan wuraren bukukuwa wato event centre da na shaƙatawa a fadin jihar.
Hakazalika hukumar ta hana kidan DJ da kuma gidajen gala yayin da aka fara azumin watan Ramadan.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.
“Daga ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026, duk irin waɗannan wurare (cibiyoyin nishaɗi) za su kasance a rufe har zuwa ƙarshen watan Ramadan mai alfarma.
“Umarnin zai fara aiki daga ƙarfe 10:00 na dare a ranar (Laraba),” in ji sanarwar.
A cewar hukumar, an ɗauki matakin ne domin bai wa al’umma damar gudanar da azumin Ramadan da ayyukan ibadarsu cikin kwanciyar hankali ba tare da wata katsalandan ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa rufewar za ta ci gaba a duk tsawon lokacin azumi, yayin da za a sanar da ranar sake buɗe wuraren, musamman a lokacin bukukuwan Sallah, a lokacin da ya dace.
Hukumar ta buƙaci dukkan masu ruwa da tsaki su ba da cikakken haɗin kai tare da bin umarnin bisa dokar da ta kafa ta.
Ta kuma jaddada cewa matakin na daga cikin aikinta na tabbatar da bin ƙa’idojin da suka shafi harkokin nishaɗi a jihar.
Hukumar ta yi addu’ar Allah Ya ba da zaman lafiya da lafiya a lokacin gudanar da ibadar watan mai alfarma, tare da roƙon Allah Ya sa kowa ya shaida watan cikin rahama da arziki.


