Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa
Published: February 18, 2026 at 4:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta bada da umarnin rufe dukkan wuraren bukukuwa wato event centre da na shaƙatawa a fadin jihar.

Hakazalika hukumar ta hana kidan DJ da kuma gidajen gala yayin da aka fara azumin watan Ramadan.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.

“Daga ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026, duk irin waɗannan wurare (cibiyoyin nishaɗi) za su kasance a rufe har zuwa ƙarshen watan Ramadan mai alfarma.

“Umarnin zai fara aiki daga ƙarfe 10:00 na dare a ranar (Laraba),” in ji sanarwar.

A cewar hukumar, an ɗauki matakin ne domin bai wa al’umma damar gudanar da azumin Ramadan da ayyukan ibadarsu cikin kwanciyar hankali ba tare da wata katsalandan ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa rufewar za ta ci gaba a duk tsawon lokacin azumi, yayin da za a sanar da ranar sake buɗe wuraren, musamman a lokacin bukukuwan Sallah, a lokacin da ya dace.

Hukumar ta buƙaci dukkan masu ruwa da tsaki su ba da cikakken haɗin kai tare da bin umarnin bisa dokar da ta kafa ta.

Ta kuma jaddada cewa matakin na daga cikin aikinta na tabbatar da bin ƙa’idojin da suka shafi harkokin nishaɗi a jihar.

Hukumar ta yi addu’ar Allah Ya ba da zaman lafiya da lafiya a lokacin gudanar da ibadar watan mai alfarma, tare da roƙon Allah Ya sa kowa ya shaida watan cikin rahama da arziki.

Labarai, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci
Next Post: Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
Isra’ila Ta Kai Hari Cibiyar Makamashin Nukiliyar Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika
  • Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.