Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato
Published: February 19, 2026 at 3:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 19, 2026

Rundunar ‘yan sandan jihar Filato tace ta tura jami’anta dake bangaren tantance bam, zuwa wurin hakar ma’adinai na kwal, a Kampanin Zurak dake karamar hukumar Wase, inda a kalla mutane talatin da bakwai suka rasa rayukansu, wassu ishirin da shida aka kai su asibiti, sanadiyyar shakar gubar gas a lokacin da suke aiki.

A wata sanarwa da ta aike wa manema labarai, rundunar ‘yan sandan a Jihar Filato tace binciken da ta fara gudanarwa ya nuna cewa guba dake cikin Ma’adanai lead oxide da sulfur da carbon monoxide ne suka hallaka masu hakar ma’adinan.

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan a jihar Filato, Alfred Alabo ya sanya wa hannu ta nuna da cewa babu alamar tashin bam a wurin, duk da haka dai jami’an sun sauki samfurin dutse da rairayi da ma’adinan dake wurin don ci gaba da bincike.

Shugaban matasan Wase, Shafi’u Sambo yace ya zuwa yanzu mutane talatin da takwas ne suka rasa ransu a wurin hakar ma’adinan na Kamfanin Zurak.

A halin da ake ciki kuma, gwamnatin jihar Filato ta jajanta wa iyalan wadanda suka rasun da kuma addu’ar sauki wa wadanda ke jinya a asibiti.

A sanarwa da komishinan yada labarai da sadarwa na jihar Filato, Madam Joyce Ramnap ta sanya wa hannu, gwamnatin tace zata karfafa dokar harkokin hakar ma’adinai don tsaron lafiyar al’umma.

Sanarwar tace gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya sha alwashin hadin gwiwa da hukumomin tarayya da sauran hukumomin dake kula da ayyukan hakar ma’adinai, kamfanoni da al’umman yankin da ake hakar ma’adinan don aiwatar da matakan kariya.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/GUBAR-GAS-YA-HALLAKA-MASU-HAKAR-MAADINAI-A-FILATO.mp3
Bidiyo, Labarai

Post navigation

Previous Post: Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Zata Rusa Gidajen Da Suke Iyakarta Da Lebanon Labarai
Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai Labarai
Rwanda Tana Keta Yarjejeniyar Zaman Lafiya – Tshisekedi Labarai
Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • Ma’aikatar Tsaron Amurka Zata Kara Samar Da Makamai Amurka
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
  • Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.