Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato
Published: February 19, 2026 at 3:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 19, 2026

Rundunar ‘yan sandan jihar Filato tace ta tura jami’anta dake bangaren tantance bam, zuwa wurin hakar ma’adinai na kwal, a Kampanin Zurak dake karamar hukumar Wase, inda a kalla mutane talatin da bakwai suka rasa rayukansu, wassu ishirin da shida aka kai su asibiti, sanadiyyar shakar gubar gas a lokacin da suke aiki.

A wata sanarwa da ta aike wa manema labarai, rundunar ‘yan sandan a Jihar Filato tace binciken da ta fara gudanarwa ya nuna cewa guba dake cikin Ma’adanai lead oxide da sulfur da carbon monoxide ne suka hallaka masu hakar ma’adinan.

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan a jihar Filato, Alfred Alabo ya sanya wa hannu ta nuna da cewa babu alamar tashin bam a wurin, duk da haka dai jami’an sun sauki samfurin dutse da rairayi da ma’adinan dake wurin don ci gaba da bincike.

Shugaban matasan Wase, Shafi’u Sambo yace ya zuwa yanzu mutane talatin da takwas ne suka rasa ransu a wurin hakar ma’adinan na Kamfanin Zurak.

A halin da ake ciki kuma, gwamnatin jihar Filato ta jajanta wa iyalan wadanda suka rasun da kuma addu’ar sauki wa wadanda ke jinya a asibiti.

A sanarwa da komishinan yada labarai da sadarwa na jihar Filato, Madam Joyce Ramnap ta sanya wa hannu, gwamnatin tace zata karfafa dokar harkokin hakar ma’adinai don tsaron lafiyar al’umma.

Sanarwar tace gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya sha alwashin hadin gwiwa da hukumomin tarayya da sauran hukumomin dake kula da ayyukan hakar ma’adinai, kamfanoni da al’umman yankin da ake hakar ma’adinan don aiwatar da matakan kariya.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/GUBAR-GAS-YA-HALLAKA-MASU-HAKAR-MAADINAI-A-FILATO.mp3
Bidiyo, Labarai

Post navigation

Previous Post: Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai
An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugabannin Kiristocin Arewa Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Ummulkhairi Afrika
  • Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
  • Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP Siyasa
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.