Ranar Alhamis, Amurka ta aza takunkumi kan kwamandoji 3 na dakarun wucin gadi a Sudan da aka fi sani da lakabin RSF a takaice, saboda rawar da suka taka kan kawanya ko zobe da suka yi wa birnin al-Fashir na tsawon shekara daya da rabi, daga bisani suka kama birnin, tana zargin su da kashe kashe masu yawan gaske.
A cikin sanarwa da Baitul Malin Amurka ta bayar Tace an aza takunkumin, ta zargi mayakan na RSF da kisan kare dangi, cin zarafin mutane, da kuma tursasa mata da lalata, a zamanin da suka yi wa birnin al-Fashir kawanya kamin daga bisani su kama birnin cikin watan oktoban bara.
Ma’aikatar kudin na Amurka ta zargi ‘yan tawayen da boye shaidar munanan ayyukan halaka rayuka da suka yi ta wajen binne binne da kuma kone kone na dubban gawarwaki.
“Amurka tana kira ga mayakan RSF su amince da tsagaita wuta na jinkai ba tare da wani bata lokaci ba. Ba zamu lamunta da ci gaba da ruruta tarzoma ba, da kashe kashen rayuka maras ma’ana a Sudan,” ministan kudin Amurka Scott Bessent ya fada a cikin sanarwar.


