Ranar Litinin, ministan harkokin wajen China yayi kira ga kasashe da suke yankin Gulf su hada kai su ki amincewa da shishshigi daga ketare, bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da harikan Iran, rikici da yanzu yake neman bazuwa a yankin.
China ta bayyana fatar kasashen da suke yankin na Gulf za su karfafa hadin kai kuma da dangantaka ta makwabta, “saboda tabbatar da ganin makomar su tana hanun su,” kamar yadda ministan harkokin wajen China Wang Yi ya fada, a tattaunawar da yayi da takwaran aikinsa na kasar Oman ta woyar tarho, kamar sanarwar da ma’aikatar harkoin wajen China ta bayar.


