Iran ta tsagaita kai hare-hare kan kasashen dake makwabtaka da ita, idan dai ba su suka kai mata hari ba.
Fadar gwamnatin Tehran ta aike da sakon bada hakuri ga makwabtan nata game da hare-haren da ta kai musu, a kokarin ta na goge fushin da makwabtan nata na kasashen tekun fasha suka yi kan harin da ta kai musu.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce yana bada hakuri ga makwabtan su, ya kuma bukace su da kada su shigar wa Amurka da Isra’ila yaki da Iran.
Ya kuma yi watsi da kiran da shugaban Amurka Donald Trump ya yi da suyi saranda, inda yace wannan mafarki ne. Shi kuma a nasa bangaren, Trump ya dauki hakurin da suka bawa sauran kasashen Gabas ta tsakiya a matsayin saranda.


