Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz
Published: March 13, 2026 at 8:01 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Iran ta bada tabbacin ci gaba da yaki tare da rufe mashigin Hormuz a matsayin abin da za ta iya kaiwa ga Amurka da Isra’ila, in ji sabon Jagoran juyin juya halin Musulunci Mojtaba Khamenei a ranar Alhamis a cikin kalaman farko da aka danganta shi da shi tun bayan da ya gaji mahaifinsa da aka kashe.

Khamenei bai bayyana da kansa ba kuma wani mai gabatarwa na gidan talabijin na kasar ne ya karanta jawabin. Ba a fitar da wani hotonsa ba tun bayan harin da Isra’ila ta kai a farkon yakin da ya yi sanadiyar mutuwar yawancin iyalansa, ciki har da mahaifinsa da matarsa.

Sanarwar ta jiya Alhamis ta dau hankali, inda Khamenei ya yi kira ga kasashen da ke makwabtaka da Iran da su rufe sansanonin Amurka da ke yankinsu tare da gargadin cewa Iran za ta ci gaba da kai musu hari.

“Ina tabbatar wa kowa da kowa cewa ba za mu yi sakaci da daukar fansar jinin shahidan ku ba,” in ji malamin nan mai tsaurin ra’ayi wanda ke da kusanci da babbar rundunar sojan Iran.

Khamenei ya kara da cewa, “Bukatar da jama’a ke da, ita ce mu ci gaba da samar da ingantaccen tsaro da kuma sanya makiya su yi nadama. Dole ne a ci gaba da yin amfani da shingen toshe mashigin ruwa na Hormuz,” Khamenei ya kara da cewa, yayin da yake magana kan hanyar jigilar kayayyaki da kashi biyar na man duniya ke bi ta gabar tekun Iran.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Da Kasashen Yamma Suna Cigaba Da Kai Ruwa Rana Akan Nukiliyar Iran
Next Post: Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar Afrika
Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.