Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya
Published: March 13, 2026 at 5:12 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya

Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri

An gargaɗi mazauna birnin Maiduguri da su guji wallafawa da kuma yaɗa labaran ƙarya a kafofin sadarwar zamani domin kauce wa haifar da tashin hankali a cikin al’umma.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya musanta rahotannin da ke yawo a kafofin sadarwar zamani da ke cewa an samu wani abu da ake kyautata zaton abin fashewa ne a harabar wani masallaci da ke unguwar Abuja Sheraton a Maiduguri.

Ya ce, “Wannan labari ba shi da tushe balle makama, domin babu wani abin fashewa da jami’an tsaro suka samu wanda zai zama barazana ga zaman lafiyar al’umma.”

Hakazalika, ya yi gargaɗin cewa, “Yaɗa bayanai marasa tushe na iya sanya mazauna birnin Maiduguri cikin firgici tare da kawo cikas ga ƙoƙarin hukumomin tsaro na tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.”

A cewarsa, “Ya kamata jama’a su riƙa tabbatar da sahihancin labarai daga amintattun majiyoyi kafin su yaɗa su a kafofin sadarwar zamani.”

Shi ma Malam Bukar Abubakar ya ce, “Akwai buƙatar jama’a su tsaftace yadda suke amfani da kafofin sadarwa domin kauce wa haddasa husuma a cikin al’umma.”

Wasu mazauna birnin, ciki har da Mathew Joshua da Ahmed Mahmud, sun ce, “Duk da matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassan jihar, akwai buƙatar jama’a su kwantar da hankalinsu tare da gujewa yaɗa rahotannin da ba a tabbatar da su ba, waɗanda ka iya ƙara dagula zaman lafiya a Maiduguri.”

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka
Next Post: Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari Afrika
  • Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri Amurka
  • Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
  • Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya Amurka
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.