Tun gabannin Amurka da Isra’ila su kaddamar hari kan Iran, Farisa mai bin tafarkin shari’a a gudanar da harkokin kasar, ta shirya nata makamin, ta wajen yin garkuwa ko shinge kan babbar hanyar da ake bi ta ruwa na safarar mai da duniya ta dogara akai a zaman nata karfi, duba da fin karfinta ta wajen makaman yaki da masu fada da ita suke dashi, kamar yadda majiyoyi da suke da masaniya kan tunani da shirye shiryen Iran suka fada.
A cikin shekaru masu yawa Iran ta sha nuna cewa, muddin kura ta kai bango, zata takaita zirga zirga a mashigin ruwan Hormuz, inda masu yakarta suke da rauni, domin duk wata kassarawar da aka samu tanan, masu yaki da ita za su ji nan da nan saboda tasirin matakin a kasuwannin makamshi a duniya baki daya.
Majiyoyin suka ce ganin yadda mashigin ruwan a yankin Gulf yake daf da setin bakin bindigar Iran, Farisa ta maida babbar albarkatun yankin a zaman garkuwarta.
Ahalinda ake ciki kuma, rahotanni sunce Iran ta bari jiragen ruwa biyu dauke da Iskar Gas kan hanyar su zuwa Indiya sun wuce ta mashigiin ruwan na Hormuz.


