Kungiyar likitoci ta kasa da kasa “Nagari Na Kowa,” da ake kira Doctors Without Borders mai cibiya a Faransa, ta fada ranar Jumma’a cewa, tayi jinyar mutane 20 sakamakon raunuka da suka samu da ya biyo bayan wani hari da aka kai da jirgin yaki da bashi da matuki, wadda ya tada gobara a wani depon mai a yammacin Sudan, wadda ya halaka mutane 11.
Harin da aka kai kan wata kasuwa da ake kira Adikong kusa da kan iyakar Sudan da Cadi a gabashin kasar, shine hari da jirgi maras matuki mafi muni a yankin a kasa da wata daya, inji kungiyar likitocin na gari na kowa, ko Doctors without Border da turancin sarauniyar Ingila, akalla mutane 11 suka kone kurmus har lahira inji Kungiyar a harin da aka kai a ranar Alhamis. Kungiyar tace a cikin mutane 23 da suka jikkata aka kai su wurinta neman jinya a Adre a Cadi har da yara bakwai.
Babban kwamishinan kare hakkin Bil’Adama na MDD Volker Turk, ya fada ranar Alhamis cewa, ofishinsa ya sami rahotannin cewa fiye da farar hula metan 200 ne suka mutu sakamakon hare haren da aka kai da jirgi da basu da matuka a Sudan. Duka sassan da suke gaba da juna a yakin, suna amfani da wadannan jirage wajen kai hare hare a yakin kasar da aka fara tun a cikin watan Afrilun 2023.
A Afirka ta kudu kuma, gwamnatin kasar ta tura sojoji samada dubu biyu domin yaki da miyagun ayyuka kasar.


