Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
Published: March 14, 2026 at 7:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar likitoci ta kasa da kasa “Nagari Na Kowa,” da ake kira Doctors Without Borders mai cibiya a Faransa, ta fada ranar Jumma’a cewa, tayi jinyar mutane 20 sakamakon raunuka da suka samu da ya biyo bayan wani hari da aka kai da jirgin yaki da bashi da matuki, wadda ya tada gobara a wani depon mai a yammacin Sudan, wadda ya halaka mutane 11.

Harin da aka kai kan wata kasuwa da ake kira Adikong kusa da kan iyakar Sudan da Cadi a gabashin kasar, shine hari da jirgi maras matuki mafi muni a yankin a kasa da wata daya, inji kungiyar likitocin na gari na kowa, ko Doctors without Border da turancin sarauniyar Ingila, akalla mutane 11 suka kone kurmus har lahira inji Kungiyar a harin da aka kai a ranar Alhamis. Kungiyar tace a cikin mutane 23 da suka jikkata aka kai su wurinta neman jinya a Adre a Cadi har da yara bakwai.

Babban kwamishinan kare hakkin Bil’Adama na MDD Volker Turk, ya fada ranar Alhamis cewa, ofishinsa ya sami rahotannin cewa fiye da farar hula metan 200 ne suka mutu sakamakon hare haren da aka kai da jirgi da basu da matuka a Sudan. Duka sassan da suke gaba da juna a yakin, suna amfani da wadannan jirage wajen kai hare hare a yakin kasar da aka fara tun a cikin watan Afrilun 2023.

A Afirka ta kudu kuma, gwamnatin kasar ta tura sojoji samada dubu biyu domin yaki da miyagun ayyuka kasar.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki
Next Post: Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
Sudan Takai Hari Kasar Chadi Da Jirgi Marar Matuki Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
  • Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
  • Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.