Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi
Published: March 17, 2026 at 4:14 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Alhamis 19 ga Maris da Juma’a 20 ga Maris, 2026 a matsayin ranakun hutun ƙasa domin bikin Ƙaramar Sallah (Eid-ul-Fitr).

Sanarwar ta fito ne ta bakin Babbar Sakatare a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani, wadda ta ce Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayar da umarnin ayyana hutun a madadin Gwamnatin Tarayya.

Ministan ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan, inda ya buƙace su da su ci gaba da riƙe kyawawan ɗabi’u da suka koyu a lokacin azumin, ciki har da soyayya, karamci, haƙuri da sadaukarwa.

Haka kuma, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwa wajen yi wa ƙasa addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai da cigaba mai ɗorewa.

Tunji-Ojo ya kuma yi kira ga jama’a da su gudanar da shagulgulan Sallah cikin natsuwa tare da miƙa hannu ga marasa galihu, domin su ma su more farin cikin wannan lokaci na ibada.

Afrika, Labarai, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
Next Post: An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko

Karin Labarai Masu Alaka

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala
  • Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato
  • Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.