Akalla mutane 18 ne aka kashe a ranar Talata a jihar Katsina, hukumomi da ‘yan sanda suka bayyana hakan, wannan harin shi ne na biyu bayan cimma wata yarjejeniya da aka yi da ‘yan ta’adda.
Jihohin Katsina da makwabta sun bi yarjejeniyoyin yin afuwa da yarjejeniyar tsaro da al’umma don shawo kan matsalar gungun ‘yan bindiga. amma har yanzu kauyukan na fuskantar hare-hare na kai-tsaye, ramuwar gayya da tashe-tashen hankula.
Hare-haren na baya-bayan nan ya fara ne lokacin da ‘yan banga suka kashe wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a kauyen Falale, lamarin da ya haifar da ramuwar gayya daga wasu ‘yan bindiga da suka kashe mutane 15 a Falale da kuma makwabtan Kadobe, in ji kwamishinan tsaro na jihar Katsina, Nasir Mua’zu.
Kakakin ‘yan sandan Katsina Abubakar Aliyu ya kuma yace harin ramuwar gayya ya yi sanadin mutuwar mutane 15.
Yayin da ake samun kananan hare-hare a makonnin da suka gabata, adadin wadanda suka mutu a harin na ranar Talata shi ne mafi girma tun ranar 3 ga watan Fabrairu, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kashe akalla mutane 21 a garin Doma da ke jihar Katsina, lamarin da ya haifar da tsagaita bude wuta na tsawon watanni shida.


