Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027
Published: March 21, 2026 at 4:08 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya | Updated: March 21, 2026

Manyan Magoya Bayan Obi Sun Fice Da Kafa Kungiyar Movement Nigeria

Wasu daga manyan jami’an siyasar dan takarar adawa a Najeriya wato Peter Obi sun barranta daga tafiyar da kafa wata kungiyar cimma sabon muradi don babban zaben 2027.

‘Yan siyasar sun koka cewa tafiyar ta su mai taken OBIDIENTS ta sauka daga kan manufofin kare martabar dimokradiyya

“A matsayinmu na masu tafiyar farar hula mun yi amanna cewa tsarin siyasa na cikin abubuwan da kan kawo cigaban kasa, za mu dage wajen hulda da wadanda su ka cancanta, cikin gaskiya da bin ka’ida ga sauran tafiyar dimokradiyya ko jam’iyyun siyasa. Wannan tafiya ce ta ma’aikata da ke fafutuka..” Inji madugun tafiyar mai taken MOVEMENT Nigeria Prince Kolade Ademola.

Ademola ya ce ba lallai a yanzu su na da wanda za su marawa baya ga babban zaben ba amma za su goyi bayan duk wanda su ka ga ya dace da tafiyarsu kuma ya karfafa cewa lokaci bai kure mu su ba.

‘Yan sabuwar tafiyar maza da mata sanya da riguna da hulunan hana-sallah masu tambarin kungiyar, na nuna rashin daidaito da tuntubar da ta dace ya sa su kaucewa tafiyar Peter Obi wanda ya zo na uku a yawan kuri’a a zaben 2023.

Mataimakin sakataren jam’iyyar LEBA na kasa wacce Obi ya yi ma ta takara Dokta Joseph Liran ya ce sam ba don dalilin kaurar Obi zuwa jam’iyyar ADC ya sa su barranta daga tafiyar ba “Obi ya na da ‘yancin shiga kowace jam’iyya mu ma mu na da namu ‘yancin”

Shi ma ma’ajin jam’iyyar LEBA Malam Hamisu Santuraki ya ce ba za su ce dole sai muradun LEBA za a bi ba a madadin ra’ayin jama’ar kasa.

Hakanan Santuraki ya ce sun kawo karshen takaddamar shugabancin jam’iyyar ta LEBA bayan hukuncin kotun koli da ya kawar da jagorancin Julius Abure.

Irin wannan tafiya ba sabon abu ba ne a shekarar siyasa inda ‘yan siyasar ke duba

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/OBIDIENTS-DUMP-OBI-START-NEW-MOVEMENT.mp3

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya
Next Post: Hawan Sallah Daga Masarautar Kaltungo

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya
Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata Afrika
Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
  • Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
  • Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
  • Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.