Kasashen larabawa da suke yankin Gulf, sun gayawa Amurka cewa, duk wata yarjejeniya da Iran, kada ya tsaya wajen kawo karshen yakin kawai, tilas ya kunshi matakai na har abada da za su gurgunta karfinta ta fuskar makamai masu linzami, da jiragen drones, da kuma, tabbatar kasar ba zata sake hana zirga zirgan jiragen ruwa a mashigin ruwa na Hormuz ba. Kamar yadda wasu majiyoyi hudu daga kasashen da suke yankin Gulf suka fada.
Shugaba Donald Trump, ya kara wa’adin da ya baiwa Iran ta bude mashigin ruwan Hormuz, inda ta nan ne kashi 20 cikin dari na mai da iskar gas da duniya take amfani da shi suke bi, ko kuma Amurka ta afkawa cibiyoyin makamashin Iran.
Amma babbar ayar tambaya da masu tsare tsare da kwararru a yankin suke fuskanta shine abunda zai biyo bayan kawo karshen yakin, wace irin makoma ce yankin zai fuskanta, kamar yadda majiyoyin hudu suka shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Jami’an kasashe da suke yankin na Gulf da Iran take harba makamai a kansu a yayin wannnan yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila akan Tehran, suna gayawa hukumomi a Washington cewa, Iran bata bar musu wata dama ko hanyar sulhu ta fuskar Diflomasiyya ba.


