China da jamhuriyar demokuradiyyar Kwango sun rattaba hanu kan wata yarjejeniya da zata zurfafa hadin kai tsakanin kasashen biyu ta fuskar hakar ma’adinai, kamar yadda gwamnatin Kwangon ta fada, yayinda gaggan kasashen duniya suke fadi tashin samun matsaya a kasar da Allah ya yiwa arzikin ma’adinai.
Kwango ce kasa dake kan gaba a duniya wajen samarda ma’adinin Cobalt, da jan karfe, ko Copper da turanci, da kuma ma’adanan da ake kira Lithium. Da coltan, wadanda aka fi amfani da su wajen harhada batura, Musamman na motoci da basa amfani da mai. Kamfanonin kasar Sin ko China sune suka mamaye wannan bangare, baya ga haka China ce babbar mai baiwa Kwango bashi.
Duk da haka, Amurka da wasu kasashe suna bukatar wadannan ma’adinai domin kera motoci da basa amfani da mai, saboda haka suma suke zawarcin hukumomin kasar da suke Kinshasa.


