Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya
Published: March 28, 2026 at 11:13 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta gudanar da babban taro na kasa inda ta amince da mukaman dukkanin shugabannin jam’iyyar ba hamayya.

Taron dai wanda shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a Abuja , ya samu halartar dukkan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar daga fadin Najeriya.

“Masu sukar cewa mu na neman maida Najeriya kasa mai bin jam’iyya daya ba haka ba ne, don ni na yi amanna da gasa a tsarin dimokradiyya amma hakan bai haramtawa kowa yin hulda da abokan siyasa ko jam’iyyar da ta kwanta ma sa a rai ba” Inji shugaba Tinubu a jawabin da ya gabatar cikin salon jawabinsa na magana daya bayan daya sannu-sannu kwana nesa.

Shugaban wanda ya nuna akwai kwarin guiwar gyaruwar lamura na kuncin tattalin arziki da a ke fuskanta, ya bukaci a yi shiru na minti daya don karrama marigayi shugaba Buhari da wani minti daya don sauran wadanda su ka kirkiro APC amma kuma sun kwanta dama.

Nan take a ka rantsar da shugabannin jam’iyyar karkashin jagorancin Nantawe Yilwatda daga jihar Filato.

Mataimakin sakataren kudi na jam’iyyar Ambasada Haruna Gimsau ya ce ba sabon abu ba ne daidaitawa wajen fidda shugabannin jam’iyya.

Ita ma mataimakiyar shugabar mata ta jam’iyyar Zainab Abubakar wacce ta sauko daga dandalin rantsarwa ta na annashuwa, ta ce hakan kwarin guiwa ne kan babban zabe na 2027.

Shugaba Tinubu ya kare gyara da a ka yi ga dokar zabe ta 2023, ya na mai caccakar ‘yan adawa da cewa ba daidai ba ne su yi korafin kan gyaran

Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana a Abuja Nasiru Adamu El-Hikaya Yana dauke da cikekken rahoto

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/APC-CONVENTION-ENDED-IN-CONSENSUS-1.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Nishadi, Siyasa

Post navigation

Previous Post: China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya
Next Post: ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila

Karin Labarai Masu Alaka

Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika
Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe Labarai
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
  • Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
  • Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
  • Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.