Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya
Published: March 30, 2026 at 9:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙasar Pakistan ta bayyana a ranar Lahadi cewa tana shirin karɓar bakuncin “tattaunawa masu ma’ana” domin kawo ƙarshen rikicin da ya shafi Iran nan da kwanaki masu zuwa, duk da cewa a baya Tehran ta zargi Amurka da shirya kai farmakin ƙasa yayin da take neman tattaunawa.

Da yake magana bayan ganawar ministocin harkokin wajen yankin, Ministan Harkokin Wajen Pakistan, Ishaq Dar, ya ce sun tattauna hanyoyin da za su iya kawo ƙarshen yaƙin cikin gaggawa da kuma na dindindin a yankin, tare da yiwuwar tattaunawa tsakanin Amurka da Iran a birnin Islamabad.

Ya ce: “Pakistan za ta ji daɗin karɓar bakunci tare da sauƙaƙa tattaunawa masu ma’ana tsakanin ɓangarorin biyu nan da kwanaki masu zuwa, domin cimma cikakkiyar sulhu mai ɗorewa kan rikicin da ke gudana.” Sai dai ba a bayyana ko Amurka da Iran sun amince za su halarci tattaunawar ba.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da White House ba su bayar da amsa nan take ba kan bukatar yin tsokaci game da yiwuwar tattaunawar a Pakistan.

A baya, Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, ya zargi Amurka da aikewa da saƙonnin tattaunawa yayin da a lokaci guda take shirin tura sojoji, yana mai ƙara da cewa Tehran a shirye take ta mayar da martani idan aka tura sojojin Amurka.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon
Next Post: Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu Afrika
Tinubu Ya Kafa Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen APC Afrika
Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki Amurka
Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
  • Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.