Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan
Published: April 2, 2026 at 2:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 2, 2026

Gwamnatin jihar Kebbi ƙarƙashin jagorancin Gwamna Nasir Idris ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da kamfanin Kaduna Electricity Distribution Company domin inganta samar da wutar lantarki a faɗin jihar.

Sakataren Gwamnatin jihar, Yakubu Bala Tafida ne ya bayyana hakan yayin da yake cikin tawagar gwamnatin jihar da ke halartar wani muhimmin taron makamashi da ke gudana a birnin London na ƙasar Birtaniya.

A cewarsa, yarjejeniyar na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na ganin an samu ingantacciyar wutar lantarki ga al’ummar Kebbi, wanda ake sa ran zai ƙarfafa harkokin tattalin arziki, jawo zuba jari, tare da inganta rayuwar jama’a.

Gwamnan ya halarci taron tare da wasu takwarorinsa da suka haɗa da Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal da Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, inda suka tattauna kan hanyoyin bunƙasa zuba jari a fannin makamashi da ci gaban yankuna.

Taron ya haɗa manyan jami’an gwamnati, ƙwararru a fannin makamashi da masu ruwa da tsaki domin lalubo hanyoyin inganta rarraba wutar lantarki a yankin da KEDCO ke aiki.

Gwamnatin Kebbi ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na inganta ababen more rayuwa da samar da yanayi mai kyau ga ci gaba, daidai da tanade-tanaden dokar lantarki ta shekarar 2023 da ke ƙarfafa shigar kamfanoni masu zaman kansu a fannin.

Gwamnatin ta kuma jaddada aniyarta na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye shiryen da za su amfani al’umma, inda wannan haɗin gwiwa a fannin lantarki ke daga cikin muhimman matakan da take ɗauka.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos
Next Post: Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
Rwanda Tana Keta Yarjejeniyar Zaman Lafiya – Tshisekedi Labarai
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe Afrika
Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Ƙarfafa Wa Sabbin Masu Ashaka Cement Gwiwar Samar Da Ayyukan Yi Afrika
  • Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
  • Tsohon Shugaban Kasa Obasanjo Ya Ziyarci IBB Siyasa
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Osun: Adeleke Ya Doke Oyebamiji, Ya Ci Gaba Da Rike Kujerar Gwamna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.