Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji
Published: April 5, 2026 at 10:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 6, 2026

Kungiyar HPV ta jihar Gombe ta shirya wani gangamin wayar da kan al’umma, inda ta hada ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya, masana ilimi, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki domin tunkarar barazanar karuwar cutar daji a jihar.

Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Muhammad Manga ya bukaci mahalarta su kirkiro dabaru masu amfani domin hana yaduwar cutar daji, musamman cutar sankarar mahaifa, da kuma yadda za a magance sauran nau’o’in cutar a cikin al’umma.

Ya bayyana cewa an hada bangarori daban-daban cikin shirin ne da gangan, musamman mambobin Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya, domin inganta tattaunawa da gano hanyoyin magance matsalolin cutar daji.

Farfesa Manga ya yaba wa mahalarta taron bisa jajircewarsu, yana mai jaddada cewa ana iya warkar da cutar daji idan aka gano ta da wuri. Ya kuma bukaci jama’a da su gaggauta neman kulawar likita idan sun lura da wasu sauye-sauye ko alamomi da ba su saba ba, tare da karfafa musu gwiwa su yada wannan sakon wayar da kai a cikin al’ummominsu.

Sauran masu jawabi, ciki har da shugabar taron, Dakta Halima Usman Farouk, Farfesa Danladi Adamu Bojude da Ferfesa Aliyu Lawal na Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe, da kuma shugabannin al’umma Musa Mustafa da Danimoh Mustafa, sun jaddada bukatar kara hadin gwiwa tsakanin ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya da sauran masu ruwa da tsaki domin yakar cutar daji yadda ya kamata.

Sun bayyana wasu daga cikin nau’o’in cutar daji da suka fi yawaita a jihar da suka hada da na mama, huhu, mafitsara ta maza, mahaifa, hanta, ciki, pankiriyas, koda, mafitsara, fata, kwakwalwa, ovaries, mahaifa ta mata da kuma esophagus.

Masu jawabin sun bukaci jama’a da su rika anfani da ayyukan kiwon lafiya da ake da su ta hanyar yin gwaje-gwaje akai-akai. Wadanda aka gano suna dauke da cutar an shawarce su da su nemi magani da wuri, yayin da sauran kuma aka karfafa musu gwiwa su yi allurar rigakafi inda ya dace.

Kungiyar ta sake jaddada kudirinta na kara fadada shirye-shiryen wayar da kai da kuma inganta samun damar ayyukan rigakafi domin rage mace-macen da ke da alaka da cutar daji a Jihar Gombe.

Daga jihar Gombe ga Rahoton Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana Aliyu Bala Gerengi

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/HPV-GOMBE.mp3
Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Najeriya, Rumbun Hotuna

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye
Next Post: Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka
  • Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna
  • Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya
  • Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida
  • Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine Amurka
  • Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
  • Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki Kiwon Lafiya
  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini Afrika
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.