Rundunar sojin Najeriya ta bayyana a jiya Lahadi cewa ta kuɓutar da wasu fararen hula 31 da aka yi garkuwa da su, inda aka kai wani hari a wata coci a Arewa maso yammacin jihar Kaduna, An kuma gano gawar mutane biyar a wurin da lamarin ya faru.
Sojin sun ce harin ya faru ne a lokacin gudanar da ibadar Easter a cocin da ke ƙauyen Ariko, a ƙaramar hukumar Kachia. Sun ƙara da cewa dakarun soji na bin sawun maharan.

Shugaban ƙungiyar Kiristoci ta (CAN) reshen jihar Kaduna, Caleb Maaji, ya ce an kai hare-hare kan majami’u biyu a ƙauyen Ariko a ranar Lahadi. Ya ƙara da cewa mutane bakwai sun mutu, yayin da adadin waɗanda aka yi garkuwa da su bai kai ga tabbatarwa ba. “Ana ci gaba da tattara bayanai,” in ji Maaji ga kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Arewacin Najeriya na fuskantar matsalar tashin hankali tsawon shekaru, ciki har da sace mutane da nufin neman kuɗin fansa da kuma hare-haren kauyuka, inda ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai ke aiki daga manyan dazuzzuka a yankin.


