Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka
Published: November 27, 2025 at 7:12 PM | By: Nafisa Ahmad

Wutar gobara mafi muni da aka gani a Hong Kong cikin shekaru fiye da 60, ta kwana tana ci, inda ya zuwa yanzu an ce akalla mutane arbain da hudu (44) ne suka mutu, yayin da ba a san inda wasu dari biyu da saba’in da tara (279) suke ba.

Har yanzu dai jami’an agaji suna ci gaba da zakulo mutane daga benayen da har zuwa safiyar nan suna ci da wuta.

‘Yan sanda sun kama mutane uku bisa zargin haddasa mutuwa dangane da wannan wuta da ta fara tashi tun jiya laraba da tsakar rana. Ya zuwa safiyar yau Alhamis agogon Hong Kong, ba a iya kashe wutar baki daya ba.

Jami’ai sun ce arba’in (40) daga cikin mutanen sun mutu a wurin ne, sauran hudu (4) kuma a asibiti. Wasu mutanen su akalla sittin da biyu (62) sun samu raunuka, wasu kunar wuta, wasu kuma shakar hayaki.

Mutanen da aka kama suna da alaka da kamfanin kwangila da ya gina benayen, inda ake tsammanin an yi amfani da wasu kayayyakin da ba su iya jure ma wuta, abinda ya saba doka.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa
Next Post: Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC

Karin Labarai Masu Alaka

Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
Ana Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Djibouti Yau Juma’a Afrika
Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
  • Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Nanata Aniyar Mallakar Greeland Daga Kasar Denmark Amurka
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.