A ranar Litinin Iran tace tana so a kawo karshen yakin da take tafkawa tsakanin ta da Isra’ila da Amurka na dindindin, ta kuma yi watsi da matsin lambar da ake mata na tayi gaggawar bude mashigin ruwa na Hormuz, ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wuta na wucen gadi, yayin da Amurka da Iran ke duba yadda za’a tsara kawo karshen yakin da akayi makonni biyar ana yi.
Iran ta aike da martanin ta, kan kudurin da Amurka ta bayar na kawo karshen yakin ta hannun kasar Pakistan, inda taki yarda da tsagaita wuta, tana mai jaddada bukatar kawo karshen yakin gaba daya, kamar yadda kafar yada labarai ta Iran ta IRNA ta fada a ranar Litinin.
Martanin da Iran ta bayar ya kunshi sharuda goma, wadanda suka hada da kawo karshen yake-yake a yankin Gabas ta tsakiya, yarjejeniyar tabbatar da wucewar jirage lafiya ta mashigin ruwa na Hormuz, cire takunkumin da aka kakaba mata, da kuma sake gina wuraren da aka rushe mata.
Shugaban Amurka Donald Trump da yayi barazanar luguden wuta kan Tehran idan ba’a cimma yarjejeniyar bude mashigin ruwa na Hormuz ba zuwa karfe takwas na daren gobe Talata ba, wato karfe 12 kenan agogon GMT, yayi watsi da kudurin na Iran, yana mai cewa wa’adin da ya bayar shine na karshe.


