Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari
Published: April 11, 2026 at 7:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta bayyana samun nasarar daure mutum 386 daga cikin mutum 508 da ake tuhuma da laifukan ta’addanci a wata gagarumar shari’ar bai daya da aka gudanar.

Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin kasar , Lateef Fagbemi (SAN), ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai ranar Juma’a. Ya bayyana cewa, Adadin Wadanda Aka Daure Mutum 386, Wadanda Aka Wanke Mutum biyu (2), Sai Wadanda Aka Sallama Mutum takwas (8).

Sauran Wadanda Ba a Kammala Nasu Ba Mutum 112, za a ci gaba da shari’arsu daga ranar 15 zuwa 18 ga watan Yuni.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa an fara wannan shari’ar ce tun ranar Talata a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Wadanda aka samu da laifin an yanke musu hukuncin zaman gidan yari daban-daban, kama daga shekara takwas (8) har zuwa daurin rai-da-rai, dangane da nauyin laifin da kowannensu ya aikata.

Fagbemi ya jaddada cewa wannan hukunci wani sako ne ga masu aikata manyan laifuka cewa Najeriya ba za ta amince da ta’addanci ba. Ya kuma jinjina wa alkalai 10 da suka sadaukar da hutunsu na Ista domin gudanar da wannan shari’a ta musamman.

Domin tabbatar da adalci da gaskiya, kungiyoyi da dama sun halarci zaman kotun a matsayin masu sanya ido, ciki har da Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA), Hukumar Kare Hakkin Dan-adam ta Kasa, Kungiyar Amnesty International, Da Wasu kungiyoyin farar hula.

Wannan shari’ar tana daya daga cikin matakai na tara (Phase 9) da gwamnati ke dauka domin dakile matsalar tsaro da kuma tabbatar da cewa wadanda aka dade ana tsare da su sun fuskanci shari’a domin maido da zaman lafiya a kasar.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu
Next Post: Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya
Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado Afrika
An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.