Tsohon jagoran masu kishin ƙasa na Hungary, Viktor Orban, ya amince da shan kaye a jiya Lahadi bayan babbar nasarar zaɓe da sabuwar jam’iyyar adawa ta Tisza ta samu, lamarin da ya zama koma baya ga abokan hulɗarsa a Rasha da kuma Fadar White House ta Shugaban Amurka Donald Trump.
Sakamakon zaɓen da aka samu bisa ƙididdigar kashi 81.5% na ƙuri’un da aka kirga ya nuna cewa jam’iyyar Tisza mai ra’ayin tsakiya ta dama kuma mai goyon bayan Tarayyar Turai (EU), ƙarƙashin jagorancin Peter Magyar, ta lashe kujeru 137, wanda ya ba ta rinjaye mai muhimmanci na kashi biyu bisa uku a majalisar dokoki mai mambobi 199, inda ta kayar da jam’iyyar Fidesz ta Orban.
“Sakamakon zaɓen bai kammala ba tukuna, amma halin da ake ciki a bayyane yake kuma a fahimce yake,” in ji Orban mai shekaru 62 a ofishin yakin neman zaɓe na Fidesz. Wasu daga cikin magoya bayansa da suka taru a wajen ofishin sun fashe da kuka yayin da suke kallonsa yana jawabi a talabijin.
Inda yace “Sakamakon zaɓen yana da raɗaɗi a gare mu, amma a bayyane yake.”


