Mutuminda ya lashe zaben a Hungary, Peter Magyar, yayi alkawari jiya Litinin cewa, zai sake dawo da tsarin demokuradiyya, da kuma ganin kungiyar tarayyar turai ta saki kudade da suka kamata ace kasar taci gajiyar su, bayan gagarumar nasarar da jam’iyyar sa ta samu kan shugaba mai barin gado wanda dan lelen ‘yan tafiyar MAGA na shugabaa Trump, kuma na kud da kud da shugaban Rasha Vladimir Putin, nasarar zata sa Hungary ta kasance mai ra’ayin tsaka tsaki ko ‘yan ba ruwana a cikin kungiyar tarayyar Turai.
Samun kashi biyu cikin uku a zaben kasar da jam’iyyar Tisza tayi a zaben da aka yi ranar lahadi, zai baiwa jam’iyyar damar karfafa tafarkin shari’a, wanda zai bude hanya da tarayyar turai ta saki biliyoyinn dala ga kasar, sai dai masu fashin baki suka ce tilas ne sabon Prime Ministan kasar ya nuna da gaske yake wajen kawo sauye sauye kamin kasar ta ci gajiyar tallafi daga tarayyar turai.


