Rundunar sojin hadin gwiwa ta Operation Hadin Kai (OPHK) da ke lura da shiyya ta biyu a Najeriya ta yi nasarar fatattakar wani gagarumin hari da ’yan ta’adda suka kai yankin Kukareta a daren Laraba wayewar Alhamis.
Harin, wanda aka fara shi jim kadan bayan tsakar dare zuwa misalin karfe 3:00 na asuba, ya gamu da tirjiya daga dakarun soji wadanda suka yi martani, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa bayan sun tafka asara mai yawa.
A cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba ya fitar a ranar 23 ga watan Afrilu, 2026, ya bayyana cewa sojoji sun yi nasarar kashe ’yan ta’adda 24 a yayin artabun.
Haka kuma, binciken da sojoji suka gudanar a fagen daga bayan kura ta lafa ya kai ga gano dimbin makaman da ’yan ta’addan suka bari, wadanda suka hada da Bindigogi kirar AK-47 guda 18 da wasu manyan bindigogi na GPMG guda 3, Bindigogin kakkabo jiragen sama (PKT) guda 2 da bututun harba bama-bamai na RPG guda 3 da na Mortar guda 2, Guruneti (Hand grenades) guda 4 da kuma dimbin alburusai.
Sanarwar ta kara da cewa sojoji biyu ne suka samu raunuka a lokacin musayar wuta, kuma tuni aka duba lafiyarsu inda suke cikin yanayi mai kyau. Kazalika, wata motar yaki ta sojoji (Tank) guda daya ta samu matsala bayan tayoyinta sun fashe a lokacin da take kai dauki.
A halin yanzu, sojoji na ci gaba da bin sawun ’yan ta’addan da suka tsere da raunuka, inda aka ga alamun jini da kayayyakin magunguna a hanyoyin da suka bi yayin gudun ceton rai.
Wannan nasara dai ta kara tabbatar da irin shirin da dakarun soji suke da shi na murkushe duk wani yunkuri na ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas, inda rundunar ta lashi takobin ci gaba da matsa lamba har sai ta kawo karshen ayyukan ta’addanci a yankin baki daya.


