Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai

Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta
Published: April 23, 2026 at 7:43 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

​Rundunar sojin hadin gwiwa ta Operation Hadin Kai (OPHK) da ke lura da shiyya ta biyu a Najeriya ta yi nasarar fatattakar wani gagarumin hari da ’yan ta’adda suka kai yankin Kukareta a daren Laraba wayewar Alhamis.

​Harin, wanda aka fara shi jim kadan bayan tsakar dare zuwa misalin karfe 3:00 na asuba, ya gamu da tirjiya daga dakarun soji wadanda suka yi martani, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa bayan sun tafka asara mai yawa.
​
A cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba ya fitar a ranar 23 ga watan Afrilu, 2026, ya bayyana cewa sojoji sun yi nasarar kashe ’yan ta’adda 24 a yayin artabun.

​Haka kuma, binciken da sojoji suka gudanar a fagen daga bayan kura ta lafa ya kai ga gano dimbin makaman da ’yan ta’addan suka bari, wadanda suka hada da ​Bindigogi kirar AK-47 guda 18 da wasu manyan bindigogi na GPMG guda 3, ​Bindigogin kakkabo jiragen sama (PKT) guda 2 da bututun harba bama-bamai na RPG guda 3 da na Mortar guda 2, ​Guruneti (Hand grenades) guda 4 da kuma dimbin alburusai.

Sanarwar ta kara da cewa sojoji biyu ne suka samu raunuka a lokacin musayar wuta, kuma tuni aka duba lafiyarsu inda suke cikin yanayi mai kyau. Kazalika, wata motar yaki ta sojoji (Tank) guda daya ta samu matsala bayan tayoyinta sun fashe a lokacin da take kai dauki.

A halin yanzu, sojoji na ci gaba da bin sawun ’yan ta’addan da suka tsere da raunuka, inda aka ga alamun jini da kayayyakin magunguna a hanyoyin da suka bi yayin gudun ceton rai.

​Wannan nasara dai ta kara tabbatar da irin shirin da dakarun soji suke da shi na murkushe duk wani yunkuri na ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas, inda rundunar ta lashi takobin ci gaba da matsa lamba har sai ta kawo karshen ayyukan ta’addanci a yankin baki daya.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
Next Post: Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe
  • Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
  • Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar Amurka
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.