Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya
Published: April 27, 2026 at 7:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta jinjina wa Masarautar Saudiyya bisa samar da gurbin karatu na kyauta ga daliban Najeriya su 50 domin karantar fannin man fetur da ma’adanan kasa.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Al’umma, Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin Jakadan Saudiyya a Najeriya, Yousef Bin Mohammed Al-Balawi, wanda ya ziyarce shi a ofishinsa da ke Abuja ranar Litinin, 27 ga watan Afrilu, 2026.

Ministan ya bayyana cewa wannan tallafin karatu ya zo daidai da burin gwamnati na bunkasa ilimi da kwarewa a fannonin da suka shafi tattalin arzikin kasa. Ya ce wannan ba gurbin karatu ba ne kawai, a’a, wani babban jari ne da za a zuba wa matasan Najeriya.

“Wannan mataki zai samar da kwararrun da Najeriya ke bukata a masana’antun man fetur da ma’adanan kasa,” in ji Ministan.

Ya kuma kara da cewa an tsara shirin ta yadda dalibai 50 za su rika amfana a duk shekara, wanda hakan zai tabbatar da dorewar shirin na dogon lokaci.

A nasa bangaren, Jakada Al-Balawi ya sanar da cewa gurbin karatun ya fito ne daga Jami’ar Man Fetur da Ma’adanai ta King Fahd (KFUPM). Ya bayyana cewa tallafin ya hada da Biyan kudin makaranta (Tuition), Tikitin jirgin sama na zuwa da dawowa, Wajen kwana kyauta, da Alawus din dake shiga hannu a kowane wata.

Jakadan ya jaddada cewa wannan kokari na nuna kyakkyawar alakar dake tsakanin kasashen biyu, yana mai cewa Saudiyya da Najeriya ginshikan tattalin arziki ne a yankunansu wadanda ke da damar bunkasa huldar kasuwanci a tsakaninsu.

Ministan ya kuma yi amfani da damar wajen bayyana jimamin Najeriya game da takaddamar dake faruwa a yankin tekun Gulf, inda ya mika sakon goyon bayan Najeriya ga kasar Saudiyya. Ya bayyana fatan samun zaman lafiya da kuma daidaita duk wata matsala ta hanyar diflomasiyya.

A karshen zaman, Ministan ya tabbatar wa jakadan cewa Najeriya za ta gaggauta aiwatar da sauran yarjeneniyoyin da aka kulla da Saudiyya, ciki har da wadanda suka shafi fannin yada labarai da sauran sassa.

Ziyarar ta samu halartar Babban Sakataren ma’aikatar, Dr. Binyerem C. Ukaire, da wasu manyan daraktoci na ma’aikatar yada labaran.

Afrika, Kimiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura
Next Post: Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji Labarai
Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
  • Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
  • Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
  • Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.