Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya
Published: April 27, 2026 at 7:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta jinjina wa Masarautar Saudiyya bisa samar da gurbin karatu na kyauta ga daliban Najeriya su 50 domin karantar fannin man fetur da ma’adanan kasa.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Al’umma, Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin Jakadan Saudiyya a Najeriya, Yousef Bin Mohammed Al-Balawi, wanda ya ziyarce shi a ofishinsa da ke Abuja ranar Litinin, 27 ga watan Afrilu, 2026.

Ministan ya bayyana cewa wannan tallafin karatu ya zo daidai da burin gwamnati na bunkasa ilimi da kwarewa a fannonin da suka shafi tattalin arzikin kasa. Ya ce wannan ba gurbin karatu ba ne kawai, a’a, wani babban jari ne da za a zuba wa matasan Najeriya.

“Wannan mataki zai samar da kwararrun da Najeriya ke bukata a masana’antun man fetur da ma’adanan kasa,” in ji Ministan.

Ya kuma kara da cewa an tsara shirin ta yadda dalibai 50 za su rika amfana a duk shekara, wanda hakan zai tabbatar da dorewar shirin na dogon lokaci.

A nasa bangaren, Jakada Al-Balawi ya sanar da cewa gurbin karatun ya fito ne daga Jami’ar Man Fetur da Ma’adanai ta King Fahd (KFUPM). Ya bayyana cewa tallafin ya hada da Biyan kudin makaranta (Tuition), Tikitin jirgin sama na zuwa da dawowa, Wajen kwana kyauta, da Alawus din dake shiga hannu a kowane wata.

Jakadan ya jaddada cewa wannan kokari na nuna kyakkyawar alakar dake tsakanin kasashen biyu, yana mai cewa Saudiyya da Najeriya ginshikan tattalin arziki ne a yankunansu wadanda ke da damar bunkasa huldar kasuwanci a tsakaninsu.

Ministan ya kuma yi amfani da damar wajen bayyana jimamin Najeriya game da takaddamar dake faruwa a yankin tekun Gulf, inda ya mika sakon goyon bayan Najeriya ga kasar Saudiyya. Ya bayyana fatan samun zaman lafiya da kuma daidaita duk wata matsala ta hanyar diflomasiyya.

A karshen zaman, Ministan ya tabbatar wa jakadan cewa Najeriya za ta gaggauta aiwatar da sauran yarjeneniyoyin da aka kulla da Saudiyya, ciki har da wadanda suka shafi fannin yada labarai da sauran sassa.

Ziyarar ta samu halartar Babban Sakataren ma’aikatar, Dr. Binyerem C. Ukaire, da wasu manyan daraktoci na ma’aikatar yada labaran.

Afrika, Kimiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano Najeriya
‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Kasashen Afirka Da Dama Suna Fafatawa Da Rasha A Yaki Da Ukraine Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya
  • UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura
  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
  • Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.