Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta jinjina wa Masarautar Saudiyya bisa samar da gurbin karatu na kyauta ga daliban Najeriya su 50 domin karantar fannin man fetur da ma’adanan kasa.
Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Al’umma, Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin Jakadan Saudiyya a Najeriya, Yousef Bin Mohammed Al-Balawi, wanda ya ziyarce shi a ofishinsa da ke Abuja ranar Litinin, 27 ga watan Afrilu, 2026.
Ministan ya bayyana cewa wannan tallafin karatu ya zo daidai da burin gwamnati na bunkasa ilimi da kwarewa a fannonin da suka shafi tattalin arzikin kasa. Ya ce wannan ba gurbin karatu ba ne kawai, a’a, wani babban jari ne da za a zuba wa matasan Najeriya.
“Wannan mataki zai samar da kwararrun da Najeriya ke bukata a masana’antun man fetur da ma’adanan kasa,” in ji Ministan.
Ya kuma kara da cewa an tsara shirin ta yadda dalibai 50 za su rika amfana a duk shekara, wanda hakan zai tabbatar da dorewar shirin na dogon lokaci.
A nasa bangaren, Jakada Al-Balawi ya sanar da cewa gurbin karatun ya fito ne daga Jami’ar Man Fetur da Ma’adanai ta King Fahd (KFUPM). Ya bayyana cewa tallafin ya hada da Biyan kudin makaranta (Tuition), Tikitin jirgin sama na zuwa da dawowa, Wajen kwana kyauta, da Alawus din dake shiga hannu a kowane wata.
Jakadan ya jaddada cewa wannan kokari na nuna kyakkyawar alakar dake tsakanin kasashen biyu, yana mai cewa Saudiyya da Najeriya ginshikan tattalin arziki ne a yankunansu wadanda ke da damar bunkasa huldar kasuwanci a tsakaninsu.
Ministan ya kuma yi amfani da damar wajen bayyana jimamin Najeriya game da takaddamar dake faruwa a yankin tekun Gulf, inda ya mika sakon goyon bayan Najeriya ga kasar Saudiyya. Ya bayyana fatan samun zaman lafiya da kuma daidaita duk wata matsala ta hanyar diflomasiyya.
A karshen zaman, Ministan ya tabbatar wa jakadan cewa Najeriya za ta gaggauta aiwatar da sauran yarjeneniyoyin da aka kulla da Saudiyya, ciki har da wadanda suka shafi fannin yada labarai da sauran sassa.
Ziyarar ta samu halartar Babban Sakataren ma’aikatar, Dr. Binyerem C. Ukaire, da wasu manyan daraktoci na ma’aikatar yada labaran.


