Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika

Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ
Published: May 9, 2026 at 1:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Tsaron Najeriya (DHQ) ta bayyana cewa dakarun kasar nan sun samu nasarar ragargazar dimbin ’yan ta’adda, inda suka kama wasu da dama tare da ceto mutum sama da 50 da aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan.

Wadannan nasarori sun faru ne a yayin ayyukan kakkaba da sojoji suka gudanar tsakanin ranar 30 ga watan Afrilu zuwa 7 ga watan Mayun 2026.

Daraktan Yada Labarai na Rundunar Tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja. Ga yadda nasarorin suke kasance a kowacce shiyya:

• Arewa maso Gabas (Operation HADIN KAI): Rundunar ta dakile hare-haren ’yan ta’adda a Magumeri da ke jihar Borno. Haka kuma, wasu daga cikin maharan sun mika wuya, yayin da aka kama masu kai musu kayan abinci da makamai.

• Arewa maso Yamma (Operation FANSAN YAMMA): Sojoji sun yi artabu da ’yan fashi a jihohin Katsina da Zamfara, inda aka kashe da dama tare da kwace babura da makamai.

• Arewa ta Tsakiya (Operation SAVANNAH SHIELD): An ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da kama masu safarar harsasai har guda 250 a cikin birnin Abuja.

• Jihar Filato: Jami’an tsaro sun bankado wata masana’antar kera makamai ba bisa ka’ida ba a Jos ta Kudu, inda aka kama mutanen da ake zargi da kera bindigogi.

• Jihar Benuwai da Kogi: An samu nasarar ceto wasu yara dalibai da aka sace daga gidan marayu.

Janar Onoja ya kara da cewa, dakarun Operation DELTA SAFE a Kudancin kasar da kuma Operation UDO KA a Kudu maso Gabas duk sun samu nasarar kama masu garkuwa da mutane da kuma dillalan makamai na kungiyar IPOB/ESN.

“Rundunar sojin kasa a karkashin jagorancin Shugaban Hafsun Tsaro, Olufemi Oluyede, ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa ’yan Najeriya sun rayu cikin lumana da kwanciyar hankali.” — Maj. Gen. Onoja

Wannan gagarumar nasara ta nuna cewa jami’an tsaro sun sake zage damtse wajen ganin sun kawo karshen matsalolin tsaro da suka addabi sassan kasar nan.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro
Next Post: Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
Amurka Da Iran Sun Cimma Yarjejeniya Tsagaita Wuta Na Makonni Afrika
Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.