Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa
Published: May 22, 2026 at 7:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Fadar Shugaban Kasar Najeriya ta karyata wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin sauya sunan Najeriya zuwa “United States of Nigeria” tare da soke dokar Shari’a a Arewacin kasar.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar 21 ga watan Mayun 2026, gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin “labarin karya” da wasu ke yadawa domin haddasa rikici da tayar da hankalin jama’a gabanin babban zaben 2027.

Sanarwar ta ce babu wani kudiri da Shugaba Tinubu ke shirin aikewa Majalisar Dokoki ta Kasa mai suna “Project True Federation” kamar yadda ake yadawa.

Fadar shugaban kasar ta zargi masu yada rahoton da kokarin haifar da rabuwar kai da rikicin siyasa a kasar.

“’Yan Najeriya su yi watsi gaba daya da wannan labari saboda masu yada shi makiyan zaman lafiya ne kuma masu neman tayar da tarzoma,” in ji sanarwar.

Gwamnatin ta kuma bayyana cewa sauya kundin tsarin mulkin kasa ba abu ne da shugaban kasa ko majalisa za su yi kai tsaye ba, domin akwai matakai masu tsauri da suka hada da samun amincewar kashi biyu bisa uku na majalisun dokokin kasar da kuma majalisun dokokin jihohi 24.

Sanarwar ta ce Shugaba Tinubu na mayar da hankali ne wajen aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziki da gwamnatin sa ta fara domin inganta rayuwar ’yan Najeriya.

Fadar shugaban kasar ta gargadi jama’a da su rika taka-tsantsan wajen karanta da yada rahotannin karya musamman yayin da harkokin yakin neman zabe ke kara karatowa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Jam’iyyar APC Ta Ayana Jamilu Gwamna A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Gombe
Next Post: APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai
Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri Amurka
  • Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.