Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
  • Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta Afrika

Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
Published: May 23, 2026 at 3:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya lashe zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress da aka gudanar a Jihar Gombe State.

Da yake sanar da sakamakon zaben, jami’in tattara kuri’u na zaben fidda gwani na shugaban kasa na APC a jihar, Gwamna Inuwa Yahaya, ya ce Shugaba Tinubu ya samu kuri’u 450,517, yayin da abokin takararsa Sterling Osifor bai samu ko kuri’a daya ba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa an gudanar da zaben cikin lumana a dukkan rumfunan zabe da kananan hukumomi goma sha daya na jihar.

Ya ce an bai wa dukkan mambobin jam’iyyar damar kada kuri’unsu ba tare da wata matsala ba, tare da jaddada cewa an gudanar da sauran zabukan fidda gwani na mukaman siyasa cikin nasara.

A nasa martanin, Shugaban APC na jihar Gombe, Mohammed Dantata Ndus, ya yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa jagoranci da yadda ya tafiyar da harkokin jam’iyyar a jihar.

Ndus ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa cewa ‘yan takarar APC a jihar za su samu nasara a zabukan gama gari masu zuwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna
Next Post: An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
Shugaban Amurka Ya Sauke Antoni Janar Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
  • Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika
  • An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.