Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
Published: June 6, 2026 at 4:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya taya Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Dr. Abubakar Shehu Abubakar III, murnar cika shekaru 12 da hawansa karagar mulkin kakanninsa.

A cikin sakon taya murnar da ya aike, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana Sarkin Gombe a matsayin amintaccen abokin hulɗa wajen gudanar da mulki, tabbatar da zaman lafiya da kuma bunkasa ci gaba, yana mai yabawa irin kyawawan halayen shugabanci da ya nuna tun bayan hawansa karagar mulki a shekarar 2014.

Gwamnan ya ce Mai Martaba Sarkin Gombe ya yi fice wajen jagoranci mai hangen nesa, hikima da sadaukarwa ga ci gaban al’ummarsa, lamarin da ya taimaka matuka wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban tattalin arziki a Jihar Gombe.

Ya kuma yaba wa Sarkin bisa rawar da yake takawa na uba ga al’umma, ayyukan alheri da kuma ƙoƙarinsa na kare da bunƙasa al’adun gargajiyar masarautar Gombe tare da ƙarfafa zaman tare cikin lumana tsakanin al’ummomi mabambanta da ke cikin masarautarsa da ma jihar baki ɗaya.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma jinjina wa Mai Martaban bisa jajircewarsa wajen tallafa wa harkokin ilimi da bunƙasa rayuwar al’umma, musamman shirye-shiryen da ke taimakawa yara marasa galihu wajen samun ingantaccen ilimi.

Har ila yau, ya yabawa Sarkin bisa jagorancinsa a matsayin Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya da Hakimai ta Jihar Gombe, inda ya ce hakan ya taimaka wajen ƙarfafa rawar da cibiyoyin gargajiya ke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba.

Yayin da yake taya Sarkin murnar wannan gagarumin ci gaba, Gwamna Inuwa Yahaya ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima da tsawon rai domin ci gaba da yi wa al’ummarsa hidima cikin nasara da albarka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
Next Post: Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika
Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi Labarai
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya Afrika
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
  • Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.