Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya taya Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Dr. Abubakar Shehu Abubakar III, murnar cika shekaru 12 da hawansa karagar mulkin kakanninsa.
A cikin sakon taya murnar da ya aike, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana Sarkin Gombe a matsayin amintaccen abokin hulɗa wajen gudanar da mulki, tabbatar da zaman lafiya da kuma bunkasa ci gaba, yana mai yabawa irin kyawawan halayen shugabanci da ya nuna tun bayan hawansa karagar mulki a shekarar 2014.
Gwamnan ya ce Mai Martaba Sarkin Gombe ya yi fice wajen jagoranci mai hangen nesa, hikima da sadaukarwa ga ci gaban al’ummarsa, lamarin da ya taimaka matuka wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban tattalin arziki a Jihar Gombe.
Ya kuma yaba wa Sarkin bisa rawar da yake takawa na uba ga al’umma, ayyukan alheri da kuma ƙoƙarinsa na kare da bunƙasa al’adun gargajiyar masarautar Gombe tare da ƙarfafa zaman tare cikin lumana tsakanin al’ummomi mabambanta da ke cikin masarautarsa da ma jihar baki ɗaya.
Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma jinjina wa Mai Martaban bisa jajircewarsa wajen tallafa wa harkokin ilimi da bunƙasa rayuwar al’umma, musamman shirye-shiryen da ke taimakawa yara marasa galihu wajen samun ingantaccen ilimi.
Har ila yau, ya yabawa Sarkin bisa jagorancinsa a matsayin Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya da Hakimai ta Jihar Gombe, inda ya ce hakan ya taimaka wajen ƙarfafa rawar da cibiyoyin gargajiya ke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba.
Yayin da yake taya Sarkin murnar wannan gagarumin ci gaba, Gwamna Inuwa Yahaya ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima da tsawon rai domin ci gaba da yi wa al’ummarsa hidima cikin nasara da albarka.


