Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika

’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata
Published: June 11, 2026 at 9:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata ’yar kasuwa a jihar Gombe ta tsallake rijiya da baya bayan wani hari da ake zargin saurayinta ya kai mata da guduma a cikin gidanta da ke unguwar Pantami a birnin Gombe.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare, lokacin da wanda ake zargin, Musa Adamu mai shekaru 35, mazaunin unguwar Riyal, ya tsallaka katangar gidan matar tare da shiga ɗakinta ba tare da izini ba.

Ana zargin ya kai mata hari da gudumar ƙarfe, sannan ya yi ƙoƙarin shaƙe ta da igiyar USB. Duk da munanan raunukan da ta samu, matar ta samu damar yin ihu domin neman taimako, lamarin da ya jawo hankalin maƙwabta tare da tilasta wa maharin tserewa daga wurin.

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta tabbatar da kama wanda ake zargin bisa laifukan yunƙurin kisa, fashi da makami da kuma jikkata mutum.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa bayan harin, jami’an ’yan sanda sun garzaya da matar zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci, inda daga bisani aka sallame ta bayan samun sauƙi.

Binciken farko da ’yan sanda suka gudanar ya nuna cewa wanda ake zargin ya taɓa neman matar ta ba shi kuɗi, amma ta ƙi amincewa da buƙatarsa, abin da ake zargin ya haddasa sabanin da ya kai ga harin.

Rundunar ta ce ta ƙwato gudumar da ake zargin an yi amfani da ita wajen kai harin da kuma igiyar USB da ake zargin an yi ƙoƙarin amfani da ita wajen shaƙe matar.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, Umar Ahmed Chosu, ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da ɗaukar tsauraran matakai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da cewa an hukunta masu aikata laifuka bisa doka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko
Next Post: ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu

Karin Labarai Masu Alaka

Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal Afrika
Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
  • Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
  • EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
  • Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.