Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
  • EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika

Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
Published: June 16, 2026 at 3:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun Soji na Sashe na biyu na oferashan FANSAN YAMMA da ke aiki a jihar Kebbi sun kwato tarin manyan makamai da kuma bama-bamai (IEDs), a wani ci gaba da ƙoƙari da nufin kawar da ta’addanci da sauran ayyukan miyagun laifuka a yankin Arewa maso Yamma.

An gudanar da wannan farmaki ne a ranar 14 ga Yuni, 2026, a yankin Dogon Daji da ke Ƙaramar Hukumar Dandi ta jihar. A yayin farmakin, jaruman dakarun sun yi amfani da ƙarfin wuta mai yawa wajen murƙushe ƙungiyar ‘yan ta’addan Lakurawa, lamarin da ya tilasta musu tserewa daga wajen.

A ci gaba da bin sawun ‘yan ta’addan da suka gudu ya kai ga gano da kwato dimbin makamai, bama-bamai da kayan aiki da suka bari a baya yayin tserewar su.

Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya ce kayan da aka kwato daga sansanin ‘yan ta’addan sun haɗa da bututun harba roka (RPG), rokokin yaƙi da dama da ake sama bututun harba roka (warheads), bama-bamai na gida (IEDs) masu yawa, babura guda biyu da ‘yan ta’addan ke amfani da su wajen kai hari, caja na batura, da wasu kayayyakin su na kashin kai.

Ya ƙara da cewa dakarun sun kammala wannan fafatawa lafiya lau, ba tare da samun asara ko jikkata ba.

Ya kuma jaddada cewa wannan nasara na nuna ƙudirin rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Yamma, oferashan FANSAN YAMMA, na rushe hanyoyin ‘yan ta’adda da ‘yan fashi da makami a yankin.

A cewarsa, Rundunar Sojin Najeriya za ta ci gaba da matsa lamba kan wadannan miyagun, tare da hana su damar gudanar da ayyukansu domin tabbatar da tsaro da lafiyar al’umma masu bin doka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
Next Post: Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya

Karin Labarai Masu Alaka

An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya
Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • GTA Hausa Logo
    Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.