Kungiyar ‘yan uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibrahim Yaqub El-Zakzaky (H) a jihar Gombe sun shiga rana ta uku na gudanar da zaman makokin Ashura, domin tunawa da shahadar Imam Hussain (AS) da iyalan gidan Manzon Allah (SAW) a filin Karbala, lamarin da ya faru a shekara ta 61 bayan hijira.
A ranar ta uku, an gudanar da wani shiri na musamman domin tunawa da Aliyul Asghar (AS), jaririn Imam Hussain (AS), wanda ya yi shahada a lokacin yaƙin Karbala.
Da yake gabatar da jawabi a wajen taron, Shugaban ‘yan uwa Musulmi a Gombe Sheikh Muhammad Abbari ya yi cikakken bayani kan yadda Aliyul Asghar ya yi shahada, tare da bayyana darussan sadaukarwa, juriya da tsayin daka da ake koya daga wannan tarihi.
Shehin malamin ya jaddada muhimmancin bin tafarkin Imam Hussain (AS) wajen kare gaskiya da adalci, yana mai kira ga mabiya da su kasance masu jajircewa a gaban zalunci da danniya.
Ya kuma yi bayani kan ƙa’idojin yaƙi a Musulunci, inda ya ce abin da aka yi wa Aliyul Asghar ya saɓa wa dokoki da ka’idojin yaƙi da addinin Musulunci ya tanada.
A yayin taron, iyaye masu jarirai sun ɗaga ‘ya’yansu a matsayin alamar tunawa da yadda Imam Hussain (AS) ya ɗaga jaririnsa a filin Karbala lokacin da yake neman a ba shi ruwa.

Mahalarta taron sun bayyana cewa wannan alama ce ta nuna biyayya ga koyarwar Imam Hussain (AS) da kuma ci gaba da bin tafarkin gwagwarmayar tabbatar da gaskiya da adalci.
An gudanar da taron cikin yanayi na jimami, addu’o’i da wa’azi, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen makokin Ashura a sassa daban-daban na jihar Gombe.


