Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
Published: July 1, 2026 at 5:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: July 1, 2026

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ƙaddamar da aikin gina babbar hanyar Akwanga–Jos–Bauchi–Gombe–Biu–Maiduguri, a wani mataki da gwamnatin tarayya ta ce zai inganta hanyoyin sufuri da bunƙasa tattalin arziki a sassan Arewacin Najeriya.

An gudanar da bikin ƙaddamar da aikin ne a garin Akwanga na jihar Nasarawa, inda Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya wakilci Shugaba Tinubu.

A cewar gwamnatin tarayya, aikin na daga cikin manyan ayyukan da ake aiwatarwa ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda, domin haɗa yankunan tekun Najeriya, savanna da yankin Sahel ta hanyar ingantacciyar hanyar mota, da nufin ƙarfafa kasuwanci, sauƙaƙa zirga-zirga da haɓaka tattalin arzikin ƙasa.

Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Yilwatda ya ce aikin ya nuna ƙudirin gwamnatin Shugaba Tinubu na samar da ingantattun ababen more rayuwa da za su haifar da ci gaban tattalin arziki, ƙarfafa haɗin kan ƙasa da kuma inganta rayuwar al’ummar Najeriya.

A nasa jawabin, Gwamnan jihar Gombe kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yabawa Shugaba Tinubu kan ba da fifiko ga ayyukan gine-ginen ababen more rayuwa.
Ya ce idan aka kammala aikin, zai haɓaka kasuwanci, rage lokacin tafiya, inganta tsaro, samar da guraben aikin yi tare da haɗa al’ummomi da kasuwanni a sassa daban-daban na ƙasar.

Shi ma Gwamnan jihar Plateau, Caleb Muftwang, ya ce al’ummar Arewacin Najeriya na yaba da yadda gwamnatin tarayya ke rabon ayyukan ci gaba cikin adalci, yana mai bayyana babbar hanyar a matsayin ɗaya daga cikin manyan ayyukan da za su kasance abin tunawa a gwamnatin Shugaba Tinubu.

A nasa ɓangaren, Ministan Ayyuka, Injiniya David Umahi, ya bayyana cewa za a aiwatar da aikin ne bisa ƙa’idojin aikin injiniya na zamani ta hannun ƙwararrun kamfanoni, yana mai cewa hakan zai inganta harkokin sufuri, rage kuɗin jigilar kayayyaki da kuma buɗe sabbin damammakin tattalin arziki ga yankunan da hanyar za ta ratsa.

Tun da farko a ranar, Gwamna Inuwa Yahaya ya halarci ƙaddamar da gadar ƙasa (Underpass) mai tsawon mita 600 da kuma sabbin hanyoyin cikin garin Akwanga, inda ya taya Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, murnar kammala ayyukan tare da yabawa gwamnatinsa bisa ƙoƙarin bunƙasa ababen more rayuwa.

Daga cikin waɗanda suka halarci bikin akwai Gwamnan jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar APC, Jamilu Isyaku Gwamna ɗan takarar gwamnan jihar Nasarawa na APC, Sanata Ahmad Aliyu Wadada da kuma sanatoci, ‘yan majalisar wakilai da sauran manyan baƙi daga jihohin Gombe, Nasarawa da Plateau.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed
Next Post: Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa

Karin Labarai Masu Alaka

Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai
Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
Rasha: Zamu Ba Gwamnatin Venezuel Gudunmawa Sauran Duniya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC Afrika
  • Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 30 A Jihar Neja Najeriya
  • Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.